• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manzon Musamman Na Shugaban Sin Ya Halarci Bikin Rantsar Da Sabon Shugaban Najeriya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Manzon Musamman Na Shugaban Sin Ya Halarci Bikin Rantsar Da Sabon Shugaban Najeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa gayyatar da gwamnatin Najeriya ta yi masa, wakilin shugaba Xi Jinping na musamman kuma mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin Peng Qinghua, ya halarci bikin rantsar da sabon shugaban Najeriya Bola Tinubu a Abuja, fadar mulkin Najeriya a ranar 29 ga watan Mayu. A jiya ne kuma shugaba Tinubu ya gana da Peng Qinghua a fadar shugaban kasa.

Peng Qinghua ya mika sakon taya murnar shugaban kasar Sin Xi Jinping ga shugaba Tinubu, inda ya ce, tun bayan kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu fiye da shekaru hamsin da suka gabata, a ko da yaushe kasashen Sin da Najeriya suna tsayawa tsayin daka kan huldar abokantaka na gaskiya, da taimakon juna, da hadin gwiwar samun nasara tare, da yin hadin gwiwa a tsakanin kasashen biyu, kuma dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ta samu ci gaba matuka.

  • Xi Jinping Ya Ziyarci Wata Makaranta Gabanin Ranar Yara Ta Duniya

Ya bayyana cewa, kasar Sin tana son yin hadin gwiwa tare da sabuwar gwamnatin Najeriya, wajen inganta dabarun raya kasa, da karfafa mu’amala a dukkan sassa, da tabbatar da goyon baya ga juna, da fadada hadin gwiwa a dukkan fannoni, da sa kaimi ga raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Najeriya zuwa mataki na gaba.

A nasa jawabin, shugaba Tinubu ya mika godiyarsa ga takwaransa na kasar Sin shugaba Xi Jinping, bisa aiko da wakilinsa na musamman don halartar bikin rantsar da shi, ya kuma bukaci Peng Qinghua da ya mika sakon gaisuwarsa ga shugaba Xi Jinping, yana mai cewa, Najeriya da Sin suna da ra’ayi iri daya, wajen gudanar da mulkin kasa, kuma ya kamata bangarorin biyu su karfafa hadin gwiwa a tsakaninsu.

Ya ce bangaren Najeriya na son kara karfafa hadin gwiwa da bangaren kasar Sin, a fannonin tattalin arziki, da kasuwanci, da tsaro, ta yadda za a ciyar da alakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi. (Mai fassarawa: Ibrahim)

Labarai Masu Nasaba

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Next Post

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Ya Zaburad Da Qausain Tv Ya Kara Himma

Related

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

10 hours ago
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan
Daga Birnin Sin

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

11 hours ago
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

12 hours ago
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

13 hours ago
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

14 hours ago
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”
Daga Birnin Sin

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

15 hours ago
Next Post
Mai Alfarma Sarkin Musulmi Ya Zaburad Da Qausain Tv Ya Kara Himma

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Ya Zaburad Da Qausain Tv Ya Kara Himma

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

September 20, 2025
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina

September 20, 2025
Sin

Yadda Ɗantsoho Ya Mayar Da Hankali Wajen Farafaɗo Da Martaba Da Ƙimar NPA

September 20, 2025
Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.