ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (4)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani and Sulaiman
4 months ago
Manzon Allah

Fadakarwa:

Muna kira ga daukacin al’ummar Musulmi kowa ya yi tanadi na musamman kar ya bari a bar shi a baya, a bana idan Allah ya kai mu watan Rabi’ul Auwal maulidin da za a yi shi ne zai zama Manzon Allah (SAW) ya cika shekaru 1,500 da haihuwa.

Yadda abin yake shi ne, idan ka dauki shekarun haihuwar Manzon Allah (SAW) 40 kafin a fara aiko masa da manzanci ka hada da shekarun da ya yi a Makkah guda 13 bayan fara saukar da manzanci zai ba ka shekaru 53. To, idan ka hada shekaru 53 da shekarar Hijira 1446 a bara, lissafin zai ba ka cewa a baran Manzon Allah (SAW) ya cika shekaru 1499 da haihuwa. A bana kuma zai zama Manzon Allah (SAW) ya cika shekaru 1,500 da haihuwa kenan.

ADVERTISEMENT

Hatta wadanda ba su yin maulidi ya kamata a bana su yi kokari su yi wani abu ko yaya kar a bar su a baya, saboda yanzu idan Allah ya ja da rayuwarmu muka ga watan Rabi’ul Auwal mai zuwa lokacin da Manzon Allah zai cika shekara 1,500 da haihuwa, to zai yi wahala mu ga lokacin da zai cika shekara 2,000 kuma. Domin da wahala a samu wani daga cikin mutanen da ke rayuwa a doron kasa yanzu ya kara wasu shekaru 500 a raye.

A lokacin da Annabi Isah (AS) ya cika shekaru 2,000 da haihuwa an ga yadda duk duniya ta dauki murna, to mu ma ya kamata Musulmi mu girgiza duniya da bukukuwa na murnar mu ma Annabinmu (SAW) ya cika shekaru 1,500 a duniya. Wannan babban alheri ne da tarihi a rayuwarmu. Allah ya hore mana dukkan abun da za mu yi hidima da shi Albarkar Annabi (SAW).

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

 

Hikimar Rashin Hade Farkon Shekarar Musulunci Da Tarihin Manzancin Annabi (SAW)

Masu karatu har yanzu dai muna kan bayani game da abubuwan da suka sa Sahabbai ba su kafa tarihin kirgen shekarar musulunci ba da wasu manyan alherai na Musulunci, sai suka zabi Muharram ta zama farkon shekarar tare da lakaba mata shekarar Hijirah.

A makon da ya gabata mun yi bayani kan hikimar ware farkon shekarar daga watan Rabi’ul Auwal zuwa watan Muharram saboda girman haihuwar Manzon Allah (SAW). A yau kuma, za mu ci gaba da bayani a kan ware kirgen farkon shekarar daban da ranar da aka fara aiken Manzanci ga Annabi (SAW).

Tun ana sauran shekara uku Manzon Allah (SAW) ya cika shekara 40 da haihuwa, ya rika fita zuwa Halwa (kadaita) a wajen garin Makka a cikin Kogon Hira, mai nisan mil shida daga cikin garin na Makka. Manzon Allah a lokacin ya bar gida, ya bar iyali, ya bar kowa domin ya kadaita da Ubangijinsa.

Wannan Kogon Hirar, lokacin da muka yi Hajji a 2004, mun ziyarci Kogon, muna yin Sallar Asuba muka fito amma ba mu kai ba sai wurin karfe takwas. Ga motoci na wucewa da komai amma kuma saboda dajin wurin ga birori ne suna ta tsalle-tsalle. To, mai karatu ka yi tunani da kwakwalwarka, a 2004 ga wasu namun daji nan har yanzu a wurin, to ina ga in an koma sama da shekara dubu daya da dari biyar, yaya wajen nan ya kasance kenan? Amma haka Annabi (SAW) zai je wajen kuma idan ya tafi ba a kasan dutsen yake zama ba sai ya hau samansa, an bar gari, an bar iyali, an bar dangi, yanzu ma an bar kan kasa ma bakidaya. Shi ma dutsen ba a zauna a sararinsa ba sai da aka shiga kogonsa, Subhanallah! In ka je hanyar shiga Kogon ma za ka ji kana hawaye saboda tafakurrin wadannan abubuwan na Manzon Allah (SAW).

Haka Annabi (SAW) yake zama a cikin Kogon, ya yi wata daya zuwa wata uku har sai abincinsa ya kare. Akwai ruwayar Sayyidina Aliyu (Karramallahu wajhahu) da ya ce idan abincin Manzon Allah ya kare shi yake kai masa. Kuma ya ce tun a wannan lokacin yakan ji wani irin kamshi a wurin wanda babu irinsa a Makka. Haka Manzon Allah ya ci gaba da yi har Hakku ya yi masa tajalli fatahi ya samu. Malaman Tafsiri kuma suka ce har Mala’ika Jibrilu ya zo masa. Ya ce masa “yi karatu”, Manzon Allah ya ce masa “ni ba mai karatu ba ne”, sai da aka yi haka sau uku kafin ayoyin nan na Suratu Ikra’a suka sauka masa (SAW). Daga nan fa sai Duniya ta yi wani irin numfashi, Manzon Allah (SAW) ya fara karantar da mu al’ummarsa da Larabci abubuwan da ya samu daga Ubanginjinsa tare da nuna mana kyawawan dabi’u.

A wannan lokacin da yake zuwa Halwa a Kogon Hira ibada ce ta Tafakkuri yake yi (Malamai sun ce da akwai wani abu da zai fi La’ilaha illallahu, zai zama Tafakkuri ne). Don haka babu wanda zai ce babu Halwa a Musulunci. Idan dai mutum zai nemi sanin hukunce-hukuncen ibada ne, ya tafi wurin Malamai, ba zai samu wannan a Halwa ba. Amma idan zai nemi sanin wani abu mai zurfi ne na Imani to wannan sai da kebancewa (Halwa).

Yanzu mutum ya yi tunani, kafin Manzon Allah (SAW) ya kawo mana addinin nan, sai da ya bar iyali, ya bar gari, ya bar kowa ya tafi kogon dutse ya yi Halwa ta shekara uku, to wani ya zo da rana tsaka ya yi shigar burtu ya ce mana ya san komai na addinin, abin da ya ga dama shi ne mai kyau, wanda bai ga dama ba haramun ne, yaushe hankali zai kama wannan ballantana imani? Ba don Rahamar Manzon Allah da ya ce ya bar mu a hanya mai sauki ba, yaushe addinin zai samu mana. Kuma dai duk da saukin addinin yana da hawa-hawa, Islam, Iman da Ihsan. Don haka ba komai na addini za ka ce ka sani ba, dole akwai iya gejinka na Islam, haka nan a Iman sannan ga kuma Ihsan ba adadi. Wani ma ya ce ba ilimin badini a cikin addini, yanzu Manzon Allah ya zauna ne a gida a gaban mata da yara addinin ya sauka? Ai sai da ya bar gida ya shiga Kogon Dutse ya yi Halwa. Kuma ba Manzon Allah shi kadai ba, sauran Annabawa ma haka ne. Har gara Kogon Hira ma a kusa yake idan aka kwatanta da Dutsen Duri Sina’a, wurin da Annabi Musa (AS) ya yi magana da Allah. Cikin dajin da mutum mai tsoro ba zai iya zuwa ba, ko a yanzu dubi yadda wurin yake balle a wancan lokacin nasu. Dubi Annabi Ibrahim, daga Isra’ila ya dauko mace da danta zai musu gida kawai amma sai da ya shafe wurin mil dubu hudu ya kawosu Makka ya ajiye. Don haka abubuwa na Annabawa da bin hanyarsu ba a sa dan karamin hankalinka a ciki.

Daga wannan Halwar ce Manzon Allah (SAW) ya zo mana da duk alheran da duniya ta sauyu da su. Larabawan da ba su iya karatu da rubutu ba suka zama Malamai. Daulolin da suka zama suna mulkar Larabawan duk suka juya suka zama a karkashinsu, sun samu yalwa na abinci maimakon gurasa da busasshen nama kawai da suke ci a da. Ko a baya-bayan nan ma, shugaban Hadaddiyar Daular Laraba (marigayi) Bin Zayed, ya roki Shehu Ibrahim Inyass (RA) ya yi musu addu’a saboda kasarsu ba ta da komai na arziki, Shehu ya ba shi Darikar Tijjaniyya ya yi masa addu’a ya ce komai zai zo muku. Su manyan kasar sun san haka kuma wasu har yau suna rike da alkawari.

 

A shekarar da aka aiko Manzon Allah (SAW), shekarar giwa tana da 40, shekarar haihuwar Annabi Isah kuma tana da 611. Allah ya ba Manzon Allah Alkur’ani wanda sai dai mu dan tsakuri abin da za mu iya a cikinsa, mu dauki zahirinsa da ya yi mana magana a kan hukunce-hukuncen ibadu da sauran mu’amaloli, sai dai mu yi wanka a bakin koginsa kawai, amma fa a Kogon Hira aka debo shi, shekara uku ana Halwa dominsa duk da karfin annabta.

Allah ya ce, wannan Alkur’anin “Littafi ne da aka saukar a gare ka (SAW) don ka fitar da mutane daga cikin duffai (mai yawa), ka shigar da su haske (guda daya) da izinin Ubangijinka (abin ba zai yiwu ba in ba izinin Ubangiji) izuwa tafarkin Mabuwayi abin godiya. Shi ne Allah mai mallakar komai da komai da ke cikin sammai da kasa”. Wannan aya sirrin aiken Manzon Allah (SAW) yana cikinta.

Wannan Alkur’ani shi ne tsarin mulkin da ya shafe kowane irin tsarin mulki duka, shi ne ya tsere wa dukkan sauran littafan da suka zo daga Allah. Ya shafe duk wani tunani na masu falsafa irinsu Aristotle, Karl Mad, da su Bictor Couzen da Khalidr Ruhi, Nepolion, William John, duk Alkur’ani ya shafe su. Haka nan duk wanda ba a cikin Alkur’anin ne zai yi tafakkuri ya fito da abubuwa ba, Alkur’ani ya shafe shi daga nan har tashin kiyama. Don haka mu so Allah, mai rahama ne, mai jinkai ne komai nasa mai sauki ne. Sannan duk mai son komai nasa ya yi dai-dai, ya debo a cikin Alkur’ani.

To duk da wadannan alherai na sirrin aike, Sahabbai sun ajiye kirgen shekarar musulunci ne da Hijirah saboda hikima.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 
Dausayin Musulunci

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

November 14, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)
Dausayin Musulunci

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025
Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
Next Post
Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

Gwamna Lawal Ya Yi Ta'aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

LABARAI MASU NASABA

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.