ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masallacin Ƙudus Na Musulmin Duniya Ne – Mabiya Shi’a

by Sulaiman
3 years ago
Masallacin kudus

A ranar Juma’a ne ’yan uwa Musulmi almajiran Sheikh Ibraheem Yaqoub El-Zakzaky, waɗanda aka fi sani da mabiya Shi’a a Nijeriya suka bi sahun ‘yan uwan su a duniya wajen gudanar da jerin-gwano don tunawa da masallacin Ƙudus. 

 

An gudanar da wannan jerin gwano a kusan duk manyan biranen ƙasar nan, wanda ya haɗa da Kaduna.

ADVERTISEMENT
  • An Yi Gangamin Nuna Goyon Bayan Falastinu A Bauchi

Ana yin jerin-gwanon duk shekara-shekara ne na goyon bayan Falasɗinawa da ake gudanarwa a ranar Juma’ar ƙarshe ta watan Ramadan don nuna goyon baya ga Falasɗinawa da adawa da Isra’ila da yahudawan sahyoniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Ana kuma gudanar da ranar Qudus a wasu ƙasashe da dama musamman a ƙasashen Larabawa da sauran ƙasashen Musulmi, inda ake gudanar da zanga-zangar nuna adawa da mamayar da Isra’ila ke yi a gabashin birnin Ƙudus. Ana gudanar da taruka a ƙasashe daban-daban na al’ummar Musulmi da ma waɗanda ba Musulmi ba a duniya.

 

A shekarar 1979 aka fara yin wannan jerin-gwano a ƙasar Iran.

 

A jawabin da wakilin mabiya Shi’a a Kaduna Kaduna ya yi, Sheikh Aliyu Tirmizi, ya ce, “mun fito ne domin nuna adawarmu ga gallaza wa al’ummar Falasɗinu da kuma mamayar da Isra’ila ke yi a birnin Ƙudus, wanda muka saba fitowa a duk ranar Juma’ar ƙarshe ta watan Ramadan.”

 

Sheikh ɗin ya kushe abubuwan da ke faruwa a ƙasar Falasɗinu, harda dawo da masallacin Al-Aqsa birnin Qudus da kuma cigaba da kashe Falasɗinawa da ƙasar Isra’ila ta ke yi.

 

Malamin ya ƙara da cewa, “muna fitowa ne cikin tsari, amma a wasu lokuta jami’an tsaro su kan far mana babu gaira, babu dalili, inda a bara sai da suka kashe mana mutane da dama. A bana ma sun far mana da hayaƙi mai sa hawaye tare da harba harsasai masu rai, inda suka harbi sama da mutum 20”.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki
Labarai

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Next Post
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Waje Ke Da Kwarin Gwiwa Game Da Kasar Sin? Baje kolin Kayayyakin Masarufi Ya Ba Da Amsa…

Me Ya Sa 'Yan Kasuwar Kasashen Waje Ke Da Kwarin Gwiwa Game Da Kasar Sin? Baje kolin Kayayyakin Masarufi Ya Ba Da Amsa…

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

November 14, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

November 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.