• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masallacin Ƙudus Na Musulmin Duniya Ne – Mabiya Shi’a

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Masallacin Ƙudus Na Musulmin Duniya Ne – Mabiya Shi’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Juma’a ne ’yan uwa Musulmi almajiran Sheikh Ibraheem Yaqoub El-Zakzaky, waɗanda aka fi sani da mabiya Shi’a a Nijeriya suka bi sahun ‘yan uwan su a duniya wajen gudanar da jerin-gwano don tunawa da masallacin Ƙudus. 

 

An gudanar da wannan jerin gwano a kusan duk manyan biranen ƙasar nan, wanda ya haɗa da Kaduna.

  • An Yi Gangamin Nuna Goyon Bayan Falastinu A Bauchi

Ana yin jerin-gwanon duk shekara-shekara ne na goyon bayan Falasɗinawa da ake gudanarwa a ranar Juma’ar ƙarshe ta watan Ramadan don nuna goyon baya ga Falasɗinawa da adawa da Isra’ila da yahudawan sahyoniya.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Ana kuma gudanar da ranar Qudus a wasu ƙasashe da dama musamman a ƙasashen Larabawa da sauran ƙasashen Musulmi, inda ake gudanar da zanga-zangar nuna adawa da mamayar da Isra’ila ke yi a gabashin birnin Ƙudus. Ana gudanar da taruka a ƙasashe daban-daban na al’ummar Musulmi da ma waɗanda ba Musulmi ba a duniya.

 

A shekarar 1979 aka fara yin wannan jerin-gwano a ƙasar Iran.

 

A jawabin da wakilin mabiya Shi’a a Kaduna Kaduna ya yi, Sheikh Aliyu Tirmizi, ya ce, “mun fito ne domin nuna adawarmu ga gallaza wa al’ummar Falasɗinu da kuma mamayar da Isra’ila ke yi a birnin Ƙudus, wanda muka saba fitowa a duk ranar Juma’ar ƙarshe ta watan Ramadan.”

 

Sheikh ɗin ya kushe abubuwan da ke faruwa a ƙasar Falasɗinu, harda dawo da masallacin Al-Aqsa birnin Qudus da kuma cigaba da kashe Falasɗinawa da ƙasar Isra’ila ta ke yi.

 

Malamin ya ƙara da cewa, “muna fitowa ne cikin tsari, amma a wasu lokuta jami’an tsaro su kan far mana babu gaira, babu dalili, inda a bara sai da suka kashe mana mutane da dama. A bana ma sun far mana da hayaƙi mai sa hawaye tare da harba harsasai masu rai, inda suka harbi sama da mutum 20”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Samun Amincewar Iyaye Kafin Shigowa Kannywood Na Da Muhimmanci -Mudassir Isyaku

Next Post

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Waje Ke Da Kwarin Gwiwa Game Da Kasar Sin? Baje kolin Kayayyakin Masarufi Ya Ba Da Amsa…

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

16 minutes ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

46 minutes ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

1 hour ago
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
Labarai

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

3 hours ago
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
Labarai

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

4 hours ago
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule
Labarai

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

5 hours ago
Next Post
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Waje Ke Da Kwarin Gwiwa Game Da Kasar Sin? Baje kolin Kayayyakin Masarufi Ya Ba Da Amsa…

Me Ya Sa 'Yan Kasuwar Kasashen Waje Ke Da Kwarin Gwiwa Game Da Kasar Sin? Baje kolin Kayayyakin Masarufi Ya Ba Da Amsa…

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.