• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masanin Najeriya da Uganda da Zambiya: Demokuradiyyar Dake Damawa Da Jama’A Wata Nasara Ce Da Jama’ar Kasar Sin Suka Samu

by CMG Hausa
3 years ago
Zambiya

Daga ranar 22 zuwa 23 ga watan Maris, an gudanar da taron kasa da kasa karo na biyu kan “Demokuradiyya: Darajoji masu muhimmanci ga daukacin bil-Adama ” a nan birnin Beijing.

Darektan cibiyar nazarin harkokin kasar Sin dake Najeriya, Charles Onunaiju ya shaidawa manema labarai a wurin taron cewa, cikakken tsarin dimokuradiyya da yake damawa da dukkan jama’a a kasar Sin, wata babbar nasara ce da jama’ar kasar Sin baki daya suka cimma karkashin jagorancin JKS. Demokuradiyya ce da ke mai da hankali kan jin dadin jama’a, da nufin ci gaba da inganta yanayin rayuwarsu.

  • Emefiele Ya Roki Gafarar ‘Yan Nijeriya Kan Matsalar Hada-Hadar Kudi Ta Intanet

Charles Onunaiju ya ce, a Afirka, muna mai da hankali sosai kan tsarin demokuradiyya da mulkin demokradiyya wanda ke jaddada dokoki, amma ba a mayar da hankali wajen taimaka wa mutane tunkarar kalubalen rayuwa. “Ina fatan dukkan kasashe, musamman kasashe masu tasowa na Afirka, za su nazarci cikakken tsarin demokuradiyyar jama’ar kasar Sin da ya kunshi jama’a a dukkan matakai, kuma su fahimci cewa, demokuradiyya ba wai kawai ta kunshi ka’idojin aiki ba ne, har ma da bukatar biyan hakikanin bukatun jama’a.”

A yayin taron, mamban hukumar kare hakkin dan Adam ta kasar Uganda Kugiza Kaheru, ya shaidawa manema labarai cewa, daukacin tsarin demokuradiyyar kasar Sin ya samo asali ne daga tushen tarihin al’adu, kuma jigonsa shi ne ci gaba da koyo, da ci gaba da koyi daga sauran sassa, da ci gaba da daidaitawa, da raya kasa, da kuma samun bunkasuwa bisa sauyi da zamani. Demokuradiyyar kasar Sin ba ta da tsauri da ra’ayin mazan jiya, amma tana da kyau wajen daidaita bukatun al’umma. Ba kawai a ka’idance ba ce, amma a aikace.

Shugaban jam’iyyar gurguzu ta kasar Zambiya, Dr Fred M’membe ya shaidawa menama labarai a yayin da yake halartar taron cewa, a kasar Sin, kana iya ganin cikakken darajar tsarin demokuradiyya, wato nuna damuwa da jin dadin bil-adama da kuma nuna damuwa ga mafi yawan jama’a, ba wai kawai masu sukuni ba.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Akwai attajirai da yawa a kasar Sin, amma ba masu arziki ne suke tsara manufofin gwamnatin kasar ba, amma bisa muhimman muradun al’ummar Sinawa. (Ibrahim Yaya)

 

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza
Daga Birnin Sin

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Next Post
Hukumar Leken Asiri Ta Amurka Ta Sake Tabka Karya Kan Batun “Nord Stream” 

Hukumar Leken Asiri Ta Amurka Ta Sake Tabka Karya Kan Batun “Nord Stream” 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

October 17, 2025
Tinubu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Shettima

‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 

October 17, 2025
Manzon Allah

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025
Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.