• English
  • Business News
Monday, September 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gargadi Gwamnatin Tarayya Kan Samar Da Karin Jami’o’i

by Sani Anwar and Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Jami’ar Gwamnatin Tarayya Kachia Ta Shirya Tsaf Domin Fara Aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ci gaba da mayar da manyan makarantun jihohi zuwa jami’o’in gwamnatin tarayya tare da sake kafa wasu sabbi da gwamnatin tarayya ke yi, na ci gaba da shan suka a wajen wasu masu ruwa da tsaki.

Adadin jami’o’in gwamnatin tarayya a wannan kasa, ya haura 63.

  • Sin Ta Mika Tallafin Wasu Jirage Marasa Matuka Na Inganta Noma Ga Kasar Zambia
  • Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

Yayin da ake kokarin daukar matakan magance yawan wadannan manyan makarantu da kuma fadada hanyoyin samun ilimi, masu suka sun yi gargadin cewa; hakan zai iya haifar da asarar samun ingantaccen ilimi.

Masu ruwa da tsakin sun jaddada cewa, idan ba a yi kokarin magance wannan matsala ba, hakan na iya kawo koma baya a fannin na ilimi, sannan kuma; ci gaba da kirkirar sabbin jami’o’in gwamnatin tarayya, na iya haifar da kara tabarbarewar harkokin ilimin a fadin wannan kasa baki-daya.

Har ila yau, masu ruwa da tsakin, sun bayyana damuwarsu kan cewa; kyautuwa ya yi a ce jami’o’in da ake da su, sun mayar da hankali wajen inganta ayyukan koyarwarsu da bincike da kuma samar da kayan ayyukan koyarwa.

Labarai Masu Nasaba

Zulum Ya Rabawa Talakawan Dikwa  Tallafin Kuɗi Da Abinci

Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

Sun kuma bayyana cewa, wajibi ne gwamnati ta mayar da hankali wajen inganta manyan makarantun da ake da su na tarayya da kuma jihohi, ta hanyar samar da wadatattun kudade, inganta abubuwan more rayuwa da kuma tabbatar da ganin ma’aikatan jami’i’on, sun samu horo na musamman da suke bukata da kuma tallafa musu.

Wani mai ba da shawara a kan harkokin binciken ilimi a Jami’ar Abuja, Humphrey Ukeaja, ya gano wasu damammaki da kalubale iri-iri da aka samu kwanan nan.

Masanin ya yi nuni da cewa, rashin samun wadatattun kudade a fannin ilimi a Nijeriya, ya zama wani babban al’amari. “Idan kuna son yin wannan sauyi misali, mayar da jami’i’o’i zuwa na gwamnatin tarayya, har yanzu a kwai ayar tambaya, shin za ku inganta su ne kokuwa inganta kudaden da za a bai wa sabbin jami’o’in? Domin kuwa, wannan ba karamin kalubale ba ne. saboda haka, gwamnati tana da kyakkyawan kudiri ne na daukar cikakken nauyin wannan ilimi?”.

Canzawa tare da kara wasu makarantu ba tare da daukar cikakken nauyinsu ba, zai sa ba za su iya tsayawa da kafafunsa, wanda a karshe ko kadan ba za a samu abin da ake nema ba na biyan bukata, in ji shi.

Farfesa Ukeaja, na da ra’ayin cewa, kafa jami’o’in tarayya a wurare kamar Kachia, zai taimaka wajen inganta ilimi tare da rage tazarar da ke tsakanin birane da kauyuka ta fannin samar da ilimi. “Don haka, idan har za a samar da jami’o’i a wuraren da suka dace, babu shakka wannan zai zama wani babban ci gaba”, in ji shi.

Ya ba da shawarar cewa, ya kamata gwamnatin tarayya ta kara yawan kudade ga fannin ilimi tare da fadada hadin gwiwa da jami’o’i masu zaman kansu, domin inganta jami’o’in, bai wa malamai horo na musamman da sauran makamantansu.
Har ila yau, kungiyar daliban Nijeriya; sun yaba da matakin, amma kuma sun nuna damuwa a kan lamarin.

Jami’in hulda da jama’a na kungiyar dalibai ta kasa (NANS), Kwamared Samson Ajasa Adeyemi, ya bayyana jin dadinsa kan kokarin da gwamnatin tarayya ke yi na magance matsalolin ilimi a Nijeriya, musamman kan yadda take mayar da makarantun jihohi zuwa na tarayya.

Sai dai ya koka da cewa, daya daga cikin manyan kalubalen da ke fuskantar fannin na ilimi a Nijeriya, ya hada da rashin isasssun kudade.

Ajasa ya yi nuni da cewa, da dama daga cikin wadannan manyan makarantun gwamnati, sun dogara ne da kudaden basussuka wajen tafiyar da makarantun, sannan akwai bukatar aiwatar da gaskiya wajen aiwatar da kasafin kudin yadda ya kamata, domin tabbatar da ganin an yi amfani da wadannan kudade yadda ya dace.

A nasa bangaren, wani dan kishin kasa, Mista Tochukwu Osuagwu, ya bukaci gwamnati ta kara zuba hannun jari a jami’o’in da ake da su, domin inganta su yadda ya kamata.

“Me zai hana a mayar da hankali wajen inganta jami’o’in da ake da su a fadin wannan kasa baki-daya, ko shakka babu, Nijeriya za ta ci gaba idan muka riki junanmu da gaskiya.

“A bayyane yake cewa, jami’o’inmu na cikin wani mummunan yanayi, wanda ba haka ya kamata al’amarin ya kasance ba, kyautuwa ya yi a ce jami’o’inmu sun samu wadatattun kayan aiki da ci gaba kamar yadda ake gani a wasu sauran kasashe”, in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Bauchi Ta Ɗage Hawan Daushe Na Sallar Bana

Next Post

Sin Ta Yi Maraba Da Ziyarar Dan Majalisar Dattawan Amurka

Related

Zulum Ya Rabawa Talakawan Dikwa  Tallafin Kuɗi Da Abinci
Labarai

Zulum Ya Rabawa Talakawan Dikwa  Tallafin Kuɗi Da Abinci

16 minutes ago
Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
Labarai

Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

1 hour ago
Yadda Ganduje Ya Janye Hannun Jarin Jihar Kano, Ya Saka Ƴaƴansa 3 A Dala Inland Dry Port
Manyan Labarai

Yadda Ganduje Ya Janye Hannun Jarin Jihar Kano, Ya Saka Ƴaƴansa 3 A Dala Inland Dry Port

3 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna Zai Dawo Aiki 1 Ga Oktoba – NRC
Labarai

Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna Zai Dawo Aiki 1 Ga Oktoba – NRC

4 hours ago
Rikicin Dangote Da PENGASSAN Ba Zai Kawo Wahalar Fetur Ba
Manyan Labarai

Rikicin Dangote Da PENGASSAN Ba Zai Kawo Wahalar Fetur Ba

6 hours ago
Gwamnan Bauchi Ya Sallami Kwamishinar Mata Daga Aiki
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Sallami Kwamishinar Mata Daga Aiki

7 hours ago
Next Post
Sin Ta Yi Maraba Da Ziyarar Dan Majalisar Dattawan Amurka

Sin Ta Yi Maraba Da Ziyarar Dan Majalisar Dattawan Amurka

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Rabawa Talakawan Dikwa  Tallafin Kuɗi Da Abinci

Zulum Ya Rabawa Talakawan Dikwa  Tallafin Kuɗi Da Abinci

September 29, 2025
Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

September 29, 2025
Yadda Ganduje Ya Janye Hannun Jarin Jihar Kano, Ya Saka Ƴaƴansa 3 A Dala Inland Dry Port

Yadda Ganduje Ya Janye Hannun Jarin Jihar Kano, Ya Saka Ƴaƴansa 3 A Dala Inland Dry Port

September 29, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna Zai Dawo Aiki 1 Ga Oktoba – NRC

Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna Zai Dawo Aiki 1 Ga Oktoba – NRC

September 29, 2025
Barcelona Ta Ɗare Kan Teburin Laliga Bayan Doke Real Sociedad

Barcelona Ta Ɗare Kan Teburin Laliga Bayan Doke Real Sociedad

September 29, 2025
Rikicin Dangote Da PENGASSAN Ba Zai Kawo Wahalar Fetur Ba

Rikicin Dangote Da PENGASSAN Ba Zai Kawo Wahalar Fetur Ba

September 29, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sallami Kwamishinar Mata Daga Aiki

Gwamnan Bauchi Ya Sallami Kwamishinar Mata Daga Aiki

September 29, 2025
Za A Gudanar Da Bikin Ajiye Furanni Don Jinjinawa Jarumai A Ranar 30 Ga Satumba

Za A Gudanar Da Bikin Ajiye Furanni Don Jinjinawa Jarumai A Ranar 30 Ga Satumba

September 28, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Dagacin Ogbayo Da Jami’an Ƴan Sa-Kai 11 A Kwara

Ƴan Bindiga Sun Kashe Dagacin Ogbayo Da Jami’an Ƴan Sa-Kai 11 A Kwara

September 28, 2025
Ana Hasashen Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Yayin Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Na Sin Zai Kai Biliyan 2.36

Ana Hasashen Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Yayin Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Na Sin Zai Kai Biliyan 2.36

September 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.