• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Za Su Yi Wa PDP Ruwan Kuri’a A Sakkwato – Farfesa A’isha Madawaki

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
PDP

A yayin da Babban Zaben 2023 ke kara karatowa, jam’iyyar PDP a Jihar Sakkwato ta bayyana cewar dimbin mata za su fito su yi wa jam’iyyar ruwan kuri’a domin tabbatar da nasarar ta a dukkanin matakai.

Mataimakiyar shugaban kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar PDP a jihar, Farfesa A’isha Madawaki Isah, ce ta bayyana hakan a yau Talata a wajen taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da aka gudanar na kananan hukumomin Gada da Goronyo a ofishin jam’iyyar a Sakkwato.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Dan Shekara 16 Kan Zargin Cin Zarafin Mai Mala Buni 
  • Buhari Ya Ba Ni Tabbacin Za A Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Atiku

Farfesa Madawaki, wadda kuma ita ce Kwamishinar Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi, ta bayyana cewar a bisa ga cikakken goyon bayan da jam’iyyar PDP ta samu a jihar da bunkasa rayuwar mata da daukacin al’umma; mata za su fito kwansu da kwarkwata su zabi PDP daga sama har kasa baki daya.

‘Yar siyasar ta bayyana cewar gwamnatin Tambuwal ta aiwatar da muhimman ayyuka masu tasiri wadanda suka bunkasa rayuwar mata, kawar da matsalolinsu da inganta jin dadinsu tare da ba su muhimman mukamai sama da kowace gwamnati a jihar.

“Za mu gudanar da yakin neman zabe tun daga rumfuna, gida-gida da kofa-kofa domin kara godiya ga ‘yan uwanmu mata kan goyon bayan da suke bai wa wannan gwamnatin tare da kara bayyana masu muhimmancin zaben PDP tun daga sama har kasa baki daya.”

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

A jawabinsa, shugaban kwamitin yakin neman zaben PDP, Tsohon Ministan Sufuri, Honarabul Yusuf Sulaiman, ya bayyana cewar jam’iyyar adawa ta APC za ta zama tarihi a zaben 2023.

Ya ce al’ummar Jihar Sakkwato za su jagoranci kakkabe mulkin APC daga sama har kasa ta hanyar tabbatar da Atiku Abubakar a matsayin shugaban kasa da Malam Sa’idu Umar a matsayin Magajin gwamna Tambuwal tare da zaben dukkanin ‘yan takarar PDP baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Mai Mala Buni Ya Bayar Da Umarnin Sakin Yaron Da Ya Ci Zarafinsa

Mai Mala Buni Ya Bayar Da Umarnin Sakin Yaron Da Ya Ci Zarafinsa

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.