Hajiya Zainab Garba, matar mataimakin gwamnan Jihar Neja, Yakubu Garba, ta rasu.
Ta rasu ne a ranar Talata a wani asibiti da ke Minna bayan ta yi fama da gajeriyar jinya.
- Farashin Man Fetur Ya Kai Naira 937 Kan Kowace Lita A Jigawa
- Sauya Fasalin Dimokuradiyyar Afirka: Lokaci Ya Yi Da Za Mu Yada Kwallon Mangwaro Mu Huta Da Kuda
A cikin sakon ta’aziyyar da babban sakataren yada labarun gwamnan jihar, Mohammed Umaru Bago, ya fitar, ya yi alhinin rasuwarta, inda ya bayyana hakan a matsayin babban rashi ga jihar.
Gwamna Bago, ya yi addu’ar Allah ya jikanta da kuma fatan Allah ya sa Jannatul-Firdaus ce makomarta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp