• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matasan Da Za A Dama Da Su A Sabuwar Gwamnati

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Matasan Da Za A Dama Da Su A Sabuwar Gwamnati
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan da Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya ratta hannu kan dokar bai wa matasa damar tsayawa takara, wannan lamari ya yi matukar zaburar da matasa wajen tashi tsaye domin shiga cikin harkokin siyasar kasar nan.

A baya dai, mafi yawancin matasa suna nuna halin ko-in-kula dangane da harkokin siyasan Nijeriya sakamakon wasu kalubale da suke fuskanta wanda ya hada da rashin kudade da kuma hana su damar shiga siyasa, amma a halin yanzu lamarin ya sauya zani.

  • Zaben Gwamna: PDP Za Ta Yi Zanga-Zangar Kwana 7 Kan Sakamakon Zaben Nasarawa 
  • ‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023

Siyasar 2023 ta zo da sabon salo, inda matasa da dama suka taka muhimmiyar rawa wajen kwato wasu kujeru daga cikin harkokin siyasar Nijeriya.

An dai samu dimbin matasa da suka samu nasarar lashe kujeru daban-daban a cikin harkokin siyasar Nijeriya a 2023. Wannan ya faru ne sakamakon tashi tsye da matasan suka yi wajen kwatan ‘yanci daga harkokin siyasar Nijeriya.

A karon farko a tarihin siyasan Nijeriya ba a taba samun lokacin da matasa suka zabura wajen shiga a dama da su a cikin harkokin siyasar kasar nan kamar wannan lokacin ba.

Labarai Masu Nasaba

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Alkaluma daga yawan masu rajistan zabe a 2023 na hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ya nuna cewa matasa su suka fi yawa a wannan lokaci. Inda matasa masu shekaru 35 da suka kai adadin kashi 70 daga cikin rajistar zabe a 2023.

Hasalima dukkan ‘yan siyasan da suka tsaya takara a zaben 2023 sun dogara ne da samun goyon bayan matasa wajen samun nasarar cin zabe, domin su ne suke da yawan masu rajista da suka kai mutum miliyan 54 daga cikin miliyan 93 da suka yi rajistar zabe.

Matasa sun yi matukar samun kwarin giwa wajen tsayawa takara da kuma zaben wadanda suke so su shugabance su, sakamakon yawan da suke da shi a harkokin siyasar 2023.

Zaben 2023 ya kasance na musamman domin shi ne farkon zaben da aka gudanar karkashin wannan sabon dokar zabe. Ko shakka babu matasan Nijeriya sun yi matukar nuna sha’arsu na shiga harkokin zabe a 2023.

A cikin jam’iyyun siyasa 18 da suka shiga takara a 2023, babu jam’iyyar da ba a samu matasa da suka tsaya takara ba tun daga kujerun ‘yan majalisa na jiha da na tarayya da gwamnoni ciki har da na shugaban kasa.

Daga cikin matasan da suka samu nasarar a zaben 2023 sun hada da:

Rukayat Shittu ‘yar shekara 26 wacce ta samu nasarar lashe zaben ‘yan majalisa jiha na mazabar Owode/Onire a karamar hukumar Asa da ke Jihar Kwara.

Rukayat ta kasance fitacciyar ‘yar jarida ta tsaya takara ne a karkashin jam’iyya mai mulki ta APC.

Ta samu kuri’u 7,521 wadda ta doke abokin takararta na jam’iyyar PDP, Abdullah Magaji wanda ya samu kuri’u 6,957.

Zababbiyar ‘yan majalisar jihar ta nuna jin dadinta lokacin da aka bayyana ta a matsayin wadda ta samu nasarar lashe zabe da za ta wakilci mazabar Owode/Onire.

Ta bayyana godiyarta ga shugabannin jam’iyyar APC a jihar da kuma masu zabe da suka ba ta wannan dama na wakiltar al’ummar mazabar Owode/Onire.

“Ana mayar da matasa da mata saniyar ware a cikin harkokin siyasar Nijeriya, amma Gwamna AbdulRahman AbdulRazak ya sauya wannan dabi’a a Jihar Kwara. Zan tabbatar na inganta tare da karfafa gwiwar matasa da mata su shiga harkokin siyasa gadan-gadan,” in ji ta.

Zababbiyar ‘yar majalisar ta kasance shugaban sashin labarai na jaridar Just Ebent ta yanar gizo.

Hakazalika, matashi dan shekara 35 mai suna Lawan Musa ya samu nasarar kwace kujerar kakakin majalisar Jihar Yobe, Hon Ahmed Mirwa Lawan a karkashin jam’iyyar PDP na mazabar Nguru II.

Zaben dai ya yi zafi sosai, inda Musa ya samu nasara da yawan kuri’u da suka kai 6,648, yayin da Lawan ya samu kuri’u 6,466.

Jami’in da ke kula da zaben, Dakta Habib Muhammad ne ya bayyana sakamakon zaben, inda ya bayyana cewa sauran ‘yan takarar da suka tsaya a jam’iyyun ADC, NNPP da APM sun samu kuri’u 3,023 da 14.

Abin lura a nan shi ne, Hon Ahmed Mirwa Lawan ya kasance dan majalisa tun a shekarar 2003 lokacin da aka zabe shi a karkashin jam’iyyar ANPP.

Shi ma babban yaron gwamnan Jihar Kaduna Nasir el-Rufai, Bello el-Ruai ya samu nasarar doke dan majalisan tarayya mai ci a mazabar Kaduna ta Arewa.

Bello ya tsaya takara ne a karkashin jam’iyyar APC wanda ya samu nasarar doke Samaila Suleiman na jam’iyyar PDP, wanda ya kasance dan majalisa mai ci da ke wakiltar mazabar Kaduna ta Arewa.

A cewar jami’in da ke kula da zaben, Farfesa Muhammed Magaji, Bello el-Rufai ya samu kuri’u 51,052, inda ya doke abokin takararsa na PDP wanda ya samu kuri’u 34,808.

Yayin da matashi mai shekaru 25, Muhammad Adamu Oyanki ya samu nasarar lashe kujerar dan majalisan jiha a mazabar Doma ta Arewa a karkashin jam’iyyar PDP.

Oyanki ya doke kakakin majalisan Jihar Nasarawa, Musa Ibrahim a zaben gwamnoni da na ‘yan jamalisar jihohi da aka kammala a makon da ya gabata.

A matsayinsa na dan shekara 25, zai kasance mafi kankantar shekaru a zauren majalisar Jihar Nasarawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MatasaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Magance Yawaitar Hatsarin Jirgin Kasa A Nijeriya

Next Post

Yadda Na’urar BBAS Ta Sauya Salon Zaben Gwamnoni

Related

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

12 hours ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

12 hours ago
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu
Manyan Labarai

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

18 hours ago
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye
Manyan Labarai

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

19 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

1 day ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

2 days ago
Next Post
Yadda Na’urar BBAS Ta Sauya Salon Zaben Gwamnoni

Yadda Na’urar BBAS Ta Sauya Salon Zaben Gwamnoni

LABARAI MASU NASABA

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.