• English
  • Business News
Tuesday, September 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matatar Ɗangote Ta Zargi Ƙungiyar PENGASSAN Da Yi Wa Al’ummar Nijeriya Zagon Ƙasa

by Sulaiman
2 hours ago
in Labarai
0
Matatar Ɗangote Ta Zargi Ƙungiyar PENGASSAN Da Yi Wa Al’ummar Nijeriya Zagon Ƙasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matatar Mai da iskar gas ta Ɗangote ta bayyana matakin yajin aikin ƙungiyar ma’aikatan kamfanonin man fetur da iskar ta ƙasa, PENGASSAN ta shiga, da cewa wani ƙoƙari ne na yi wa tattalin arzikin Nijeriya da ci gaban al’ummar ta zagon ƙasa, kamar yadda jaridar matattarar labarai ta rahoto.

 

A ranar Litinin ne ƙungiyar ta PENGASSAN ta shiga yajin aiki na sai baba ta gani saboda matakin matatar Ɗangoten na korar wasu ma’aikatan ta kimanin 800.

  • Ma’aikatan Jinya Sun Yaba Wa Gwamnatin Kaduna Kan Aiwatar Da Sabon Tsarin Albashi
  • Xi Jinping Ya Halarci Bikin Tunawa Da Mazan Jiya

Ita kuma matatar, a cikin wata sanarwa da ta fitar, ta bayyana cewa, ta sallami ma’aikatan ne a wani mataki na ƙoƙarin daidaita tsarin aikin matatar.

 

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ba Ta Da Sarƙaƙiyar Jagoranci Idan Ta Samu Shugabanni Masu Gaskiya – Obasanjo 

Ma’aikatan Jinya Sun Yaba Wa Gwamnatin Kaduna Kan Aiwatar Da Sabon Tsarin Albashi

Ɓangarorin biyu sun tashi baran-baran a wata tattaunawar da suka yi ƙarƙashin jagorancin Ministan ƙwadago na Nijeriya, Mohammed Dingyadi a ranar Litinin.

 

Wannan yajin aiki na PENGASSAN ya shafi rufe ɓangarori da dama na harkar mai a Nijeriya, ciki kuwa har da babban kamfanin mai na ƙasa, NNPCL, tare da dakatar da ba matatar Ɗangote ɗanyen mai.

 

Kungiyar ta PENGASSAN ta ja daga, inda ta bayyana cewa, “Muna kan bakar mu har yanzu, saboda mutanen mu da aka kora daga aiki, muna so dole a mayar da su.”

 

Wannan na zuwa ne a yayin da wata kotun Abuja ta bayar da umarnin hana yajin aikin ƙungiyar ta PENGASSAN da ɗaukar matakin hana kai wa matatar Ɗangote ɗanyen mai da iskar gas.

 

Matatar Ɗangote ce ta shigar da ƙarar a gaban kotun ma’aikata a Abuja, kuma Alƙalin kotun ya ce Matatar Ɗangote kamfani ne mai zaman kansa da ke da lasisin samarwa da raba man fetur domin buƙatun ‘yan Nijeriya.

 

Sai ga shi kuma duk da umarnin kotun, ƙungiyar ƙwadago ta NLC a Nijeriya ta yi barazanar shiga yajin aikin domin nuna goyon baya ga PENGASSAN.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Kimiyya Da Fasaha

Next Post

Sin Ta Fitar Da Kundi Mai Kunshe Da Matsayinta Dangane Da Kudurin MDD Mai Lamba 2758

Related

Obasanjo
Labarai

Nijeriya Ba Ta Da Sarƙaƙiyar Jagoranci Idan Ta Samu Shugabanni Masu Gaskiya – Obasanjo 

3 hours ago
Ruwa
Labarai

Ma’aikatan Jinya Sun Yaba Wa Gwamnatin Kaduna Kan Aiwatar Da Sabon Tsarin Albashi

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Biyan Ƙarin ₦32,000 Ga ‘Yan Fansho
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Biyan Ƙarin ₦32,000 Ga ‘Yan Fansho

7 hours ago
Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

8 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Ta Sace Kwamishinan Zaɓe A Neja, Tsohon Shugaban SUBEB, Da Wasu

11 hours ago
Bam Ya Hallaka ‘Yan Sa-kai Biyu A Yobe
Labarai

Bam Ya Hallaka ‘Yan Sa-kai Biyu A Yobe

13 hours ago
Next Post
Sin Ta Fitar Da Kundi Mai Kunshe Da Matsayinta Dangane Da Kudurin MDD Mai Lamba 2758

Sin Ta Fitar Da Kundi Mai Kunshe Da Matsayinta Dangane Da Kudurin MDD Mai Lamba 2758

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Sin Mai Inganci Ya Samar Da Damammaki Ga Duniya

Ci Gaban Sin Mai Inganci Ya Samar Da Damammaki Ga Duniya

September 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Kundi Mai Kunshe Da Matsayinta Dangane Da Kudurin MDD Mai Lamba 2758

Sin Ta Fitar Da Kundi Mai Kunshe Da Matsayinta Dangane Da Kudurin MDD Mai Lamba 2758

September 30, 2025
Matatar Ɗangote Ta Zargi Ƙungiyar PENGASSAN Da Yi Wa Al’ummar Nijeriya Zagon Ƙasa

Matatar Ɗangote Ta Zargi Ƙungiyar PENGASSAN Da Yi Wa Al’ummar Nijeriya Zagon Ƙasa

September 30, 2025
Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Kimiyya Da Fasaha

Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Kimiyya Da Fasaha

September 30, 2025
Obasanjo

Nijeriya Ba Ta Da Sarƙaƙiyar Jagoranci Idan Ta Samu Shugabanni Masu Gaskiya – Obasanjo 

September 30, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Wanzar Da Zamanantarwa Irin Ta Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Wanzar Da Zamanantarwa Irin Ta Sin

September 30, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Tunawa Da Mazan Jiya

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Tunawa Da Mazan Jiya

September 30, 2025
Ruwa

Ma’aikatan Jinya Sun Yaba Wa Gwamnatin Kaduna Kan Aiwatar Da Sabon Tsarin Albashi

September 30, 2025
Ya Kamata a Nace Ga Ka’idojin MDD Duk Da Kalubalen Da Ake Fuskanta

Ya Kamata a Nace Ga Ka’idojin MDD Duk Da Kalubalen Da Ake Fuskanta

September 30, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Biyan Ƙarin ₦32,000 Ga ‘Yan Fansho

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Biyan Ƙarin ₦32,000 Ga ‘Yan Fansho

September 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.