• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Sama Da Limamai Da Fastoci 30 Suka Halarci Buda Bakin Azumin Da Aka Yi A Kaduna Kan

by Bashir Bello, Abuja
3 years ago
Tsaro

Lokacin da ake buda bakin azumin kan matsalar tsaro

Sama da Limamai da Fastoci 30 suka halarci taron Bude baki na azumin da aka yi domin neman Allah ya kawo dauki kan matsalar tsaro da sauran abubuwan da suka addabi Jihar Kaduna wanda dan takarar gwamnan jihar a karkashin jam’iyyar APC, Hon. Mohammed Sani Sha’aban ya yi kiran a yi a jiya Litinin.

A bisa yunkurin da Hon. Sha’aban yake yi na ganin an samu nasarar kawo karshen duk wata ukuba da halin kuncin rayuwa a Jihar Kaduna, ya nemi a yi azumin inda dimbin al’umma suka amsa kira domin neman daukin Ubangiji dangane da yanayin halin rayuwa da al’ummar Jihar su ke ciki.

  • Adamu Yaki Cewa Uffan Kan Mika Sunan Lawan Da Akpabio Ga INEC

An gudanar da taron bude baki na shan ruwan Azumin ne a ofishin kamfen dan takarar dake garin Kaduna.

Da yake jawabi a wajen taron bude bakin Azumin, Dan takarar kuma Danburan Zazzau Sani Sha’aban, ya bayyana cewa wannan wani mataki ne da suka dauka domin neman kawo karshen halin ha’ula’i da al’ummar Jihar ke ciki sakamakon irin yadda al’amura na rashin kwanciyar hankali suke kasancewa.

Ya kara da cewa al’ummar Jihar ba su da wani karfi wanda ya wuci karfin Ubangiji kuma a dalilin hakan ne suka gudanar da wannan Azumin na musamman domin neman samun sauki a cikin rayuwar su da al’amuran Jihar Kaduna wanda hakan ke neman salwantar da rayuwar al’ummar.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

“Ni mutumin Zariya ne kuma daga Zariya na Fito, kuma yanzu haka akalla sama da mutane Miliyan daya suka gudanar da wannan Azumin wanda mu ka yi bude baki a nan cikin cikin garin Kaduna.”

“Kuma a cikin garin Kaduna akalla sama da mutane Miliyan daya suka gudanar da wannan Azumin, haka a garin Zankuwa, Kafanchan da Kachia kuma muna saran Allah Zai dubi al’amuran mu ta hanyar da zamu samu saukin rayuwa.

Tsaro
Hon. Sha’aban yana gaisawa da wasu mahalarta buda bakin

Acewarsa, wasu da dama daga cikin al’ummar Jihar sun rasa ayyukan su, a yayin da wasu matasa suka kasa yin karatu sakamakon karin kudin wanda hakan yasa iyayensu basa iya biyan kudin makarantarsu.

Ya ci gaba da cewa akalla kusan kwanaki casa’in kenan da aka yi garkuwa da yan Uwansu wadanda suka hada da Sadiq Ango Abdullahi, MS Ustaz da sauran al’umma a harin Jirgin Kasa, to amma har yanzu Gwamnatin ta kasa yin komai domin ganin an sako su.

Honarabul Sha’aban, ya kara da cewa ya shigar da kara kotu domin neman hakkin shi a bisa karfa-karfan da aka yi masa a lokacin zaben fidda gwani na Jam’iyyar ta APC, kana ya aika da sakon neman ita Uwar Jam’iyyar ta dauki matakin da ya dace na ganin cewa ta daidaita al’amura a tsakanin duka Ya’yan Jam’iyyar.

  • https://leadership.ng/just-in-terrorists-attack-kaduna-church-kill-3-worshippres-abduct-many/

Hakazalika, ya yi nuni da cewa masu zaben ‘yan takara mutane 1224 da suka sayi fom din zama masu zaben yan takara ba a basu dama ba, su ma sun shigar da kara kotu domin neman hakkin su bisa rashin adalcin da aka yi musu da tauye musu hakki a lokacin zaben.

A karshe, Sani Sha’aban, ya bayyana cewa suna sa ran wannan Azumin da suka gudanar kuma su kayi tawassali da ita, zai zame musu wata silla na samun waraka bisa duk wata damuwar da ta addabe su a ciki da wajen Jihar ta Kaduna.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Zargin Cin Hanci: PDP Ta Janye Kalamanta, Ta Nemi Afuwar Gwamnan Kwara

Zargin Cin Hanci: PDP Ta Janye Kalamanta, Ta Nemi Afuwar Gwamnan Kwara

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.