• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Sama Da Limamai Da Fastoci 30 Suka Halarci Buda Bakin Azumin Da Aka Yi A Kaduna Kan

by Bashir Bello, Abuja
3 years ago
in Labarai
0
Tsaro

Lokacin da ake buda bakin azumin kan matsalar tsaro

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sama da Limamai da Fastoci 30 suka halarci taron Bude baki na azumin da aka yi domin neman Allah ya kawo dauki kan matsalar tsaro da sauran abubuwan da suka addabi Jihar Kaduna wanda dan takarar gwamnan jihar a karkashin jam’iyyar APC, Hon. Mohammed Sani Sha’aban ya yi kiran a yi a jiya Litinin.

A bisa yunkurin da Hon. Sha’aban yake yi na ganin an samu nasarar kawo karshen duk wata ukuba da halin kuncin rayuwa a Jihar Kaduna, ya nemi a yi azumin inda dimbin al’umma suka amsa kira domin neman daukin Ubangiji dangane da yanayin halin rayuwa da al’ummar Jihar su ke ciki.

  • Adamu Yaki Cewa Uffan Kan Mika Sunan Lawan Da Akpabio Ga INEC

An gudanar da taron bude baki na shan ruwan Azumin ne a ofishin kamfen dan takarar dake garin Kaduna.

Da yake jawabi a wajen taron bude bakin Azumin, Dan takarar kuma Danburan Zazzau Sani Sha’aban, ya bayyana cewa wannan wani mataki ne da suka dauka domin neman kawo karshen halin ha’ula’i da al’ummar Jihar ke ciki sakamakon irin yadda al’amura na rashin kwanciyar hankali suke kasancewa.

Ya kara da cewa al’ummar Jihar ba su da wani karfi wanda ya wuci karfin Ubangiji kuma a dalilin hakan ne suka gudanar da wannan Azumin na musamman domin neman samun sauki a cikin rayuwar su da al’amuran Jihar Kaduna wanda hakan ke neman salwantar da rayuwar al’ummar.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

“Ni mutumin Zariya ne kuma daga Zariya na Fito, kuma yanzu haka akalla sama da mutane Miliyan daya suka gudanar da wannan Azumin wanda mu ka yi bude baki a nan cikin cikin garin Kaduna.”

“Kuma a cikin garin Kaduna akalla sama da mutane Miliyan daya suka gudanar da wannan Azumin, haka a garin Zankuwa, Kafanchan da Kachia kuma muna saran Allah Zai dubi al’amuran mu ta hanyar da zamu samu saukin rayuwa.

Tsaro
Hon. Sha’aban yana gaisawa da wasu mahalarta buda bakin

Acewarsa, wasu da dama daga cikin al’ummar Jihar sun rasa ayyukan su, a yayin da wasu matasa suka kasa yin karatu sakamakon karin kudin wanda hakan yasa iyayensu basa iya biyan kudin makarantarsu.

Ya ci gaba da cewa akalla kusan kwanaki casa’in kenan da aka yi garkuwa da yan Uwansu wadanda suka hada da Sadiq Ango Abdullahi, MS Ustaz da sauran al’umma a harin Jirgin Kasa, to amma har yanzu Gwamnatin ta kasa yin komai domin ganin an sako su.

Honarabul Sha’aban, ya kara da cewa ya shigar da kara kotu domin neman hakkin shi a bisa karfa-karfan da aka yi masa a lokacin zaben fidda gwani na Jam’iyyar ta APC, kana ya aika da sakon neman ita Uwar Jam’iyyar ta dauki matakin da ya dace na ganin cewa ta daidaita al’amura a tsakanin duka Ya’yan Jam’iyyar.

  • https://leadership.ng/just-in-terrorists-attack-kaduna-church-kill-3-worshippres-abduct-many/

Hakazalika, ya yi nuni da cewa masu zaben ‘yan takara mutane 1224 da suka sayi fom din zama masu zaben yan takara ba a basu dama ba, su ma sun shigar da kara kotu domin neman hakkin su bisa rashin adalcin da aka yi musu da tauye musu hakki a lokacin zaben.

A karshe, Sani Sha’aban, ya bayyana cewa suna sa ran wannan Azumin da suka gudanar kuma su kayi tawassali da ita, zai zame musu wata silla na samun waraka bisa duk wata damuwar da ta addabe su a ciki da wajen Jihar ta Kaduna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mahaifiyar Dan Takarar Sanatan Jigawa Ta Tsakiya

Next Post

Zargin Cin Hanci: PDP Ta Janye Kalamanta, Ta Nemi Afuwar Gwamnan Kwara

Related

Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

15 minutes ago
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
Labarai

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

3 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

4 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

6 hours ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

9 hours ago
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet
Manyan Labarai

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

10 hours ago
Next Post
Zargin Cin Hanci: PDP Ta Janye Kalamanta, Ta Nemi Afuwar Gwamnan Kwara

Zargin Cin Hanci: PDP Ta Janye Kalamanta, Ta Nemi Afuwar Gwamnan Kwara

LABARAI MASU NASABA

Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

June 3, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

June 3, 2025
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

June 3, 2025
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.