• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maza Ne Ke Da Laifin Yawaitar Mace-macen Aure A Arewacin Nijeriya —Fatima Lawal

by Basira Nakura
2 years ago
in Zamantakewa
0
Maza Ne Ke Da Laifin Yawaitar Mace-macen Aure A Arewacin Nijeriya —Fatima Lawal

Fatima Lawal

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau mun kawo muku hirar da muka yi da wata hazika, Malama data shahara wajen tarbiyartar tare da ba mata shawarar yadda za su yi zaman aurensu ba tare da wata matsala ba, wato Hajiya Fatima Lawan.

Ga dai yadda hirara ta kasance kamar yadda wakiliyarmu Basira Nakura ta nakalto mana.

  • An Gurfanar Da Matashi A Kotu Sakamakon Lakadawa Dan Sanda Dukan Kawo Wuka
  • Taron Jagororin JKS Ya Jaddada Aiwatar Da Shawarwari Da Tsare-tsaren Babban Taron Wakilan Jam’iyyar Karo Na 20 Cikin Hadin Kai 

Da farko masu karatu za su so jin cikakken sunan ki da tarihinki a takaice

Sunana Fatima Lawan Alima”a rufa bi Tasallah Nabilusi Bako  wancan sunan mahaifi nane wannan kuma sunan mijina nane saboda wasu suna tunanin sunan mahaifi nane a’a sunan mijina Nabilisi Bako mahaifina shi ne Muhammad Lawan Ali

Tarihin rayuwata ni na taso ‘yar gidan makaranta ce saboda haka nataso a matsakaici ‘yar rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan

Na yi karatun firamare dana sakandire koda yake jarrabawar da muka dauka a iya kokarin da mukai basu bamu takarda ba sai suka daukemu makarantar muka zana jarrabawa daga nan sai na shiga makarantar Legal wacce take makaranta ce ta koyon addinin Musulunci. Wannan kenan, na yi Difloma na yi Adbas a  bangaren Nizaniya ma’ana wato (Na zamani kenan)

Amma a bangaren na addinin musulunci wanda ya fara bani ilimi shine mahaifina daga nan sai aka samu  makarantar Allo sai kuma muka shiga makarantar islamiyya ta Malam Shehu Alkali wadda dama daga ita ne muka shiga makarantar gaba da firamare inda daga ita ne naci makarantar W.A.T.C  wacce a lokacin take a Sharada, To amma ban samu zuwa ba sai aka yi min aure, lokacin da aka zo neman auren ne Mahaifina ya yi kokarin nuna musu cewar shi  ya so in yi karatu mai dan zurfi, to amma da yake Allah ya nufa da aka kaini gidana, kasan cewar gidan da aka kaini gidan makaranta ne bangaren gidan uwar mijina gidan Malam Abubakar Ramadan, gidan kuma mahaifinsa shi ne gidan Alhaji Bako Mai Turare

Saboda haka ya yi kokarin ɗorani akan wannan harka ta ilimin addinin Musulunci

To Daga nan kuma sai aka zo duba da cewar nataba koyarwa tun ina da shekara goma a makarantar islamiyyar mu

Duba da Nazarin da malaman mu sukai sukaga cewar zamu iya rike hakan, daga nan mahaifin mai gida  suka yi kwamiti don ganin cewar ana samun raunin ilimin mata a Jihar Kaduna aka yi  a lokacin da aka yi wata jarrabawa ta tafiya Hajji aka ce sai masu karatu ne  za su tafi sai Kano mata suka dinga fadowa -dan haka sai  iyayen mu mazanmu  ko yayyensu zance suka kafa wani  kwamiti sukaga  ya kamata lallai a baiwa   mata  ilimin  bangaren addinin Musulunci dan suma sudinga haye Tambayoyi  kamar yadda Kaduna suke yi lokacin,

Don haka da aka kafa kwamnatin sai aka sa da mazanmu sai suka ga cewar yakamata a samu wadanda za su dinga yi, take Maigidana ya ce ya bada arona duba da ganin cewar na taba karantarwa a baya sai mahaifinsa ya ce to itama karatun nata kadanne amma zamu bayar da ita kafin a samu wasu to daga nan aka dore.

To  sai mahaifin mijina ya soma bani karatu wanda a silar wannan muka soma bude makarantu na mata mun fara da ta kwamiti to daga karshe abin yanayi da kadan da kadan karshe ma abin ya  dawo hannuna gaba daya.

To sai ya kasance muna ta bude rassa a takaice, hakika mun samu cigaba da taimako  sosai musamman ta bangaren mahaifin Mai Gidana ya bani karfin gwiwa sosai kuma ya yi wa mijina jan kunnen da gargadin kada ya ce zai hanani matukar rayuwarsa don haka duk inda zan je in bude raeshe ko in bada gudunmawa Mai gidana baya hanani.

A haka muka samu karatuttukan da muka yi wanda har ta kai takawomu ga matsayin da muke kai wanda a’umma take gani.

Taya kike iya fuskantar matsalolin mata  Duba yadda kike mu’amala da mata ma bammanta wannan za ta zo ta ce miki ga matsalar ta waccan ma tac e miki ga matsalarta, ga yawan mace-macen aure a kasar Hausa ko meye yake janyo haka?

To Gaskiya mace-macen aure ya kan faru ne ta Rashin Hakuri da Rashin Ma’auratan basa duba tsakanin ko wane bangaren mazan da matan basa duba da yadda yanayin rayuwar da ake ciki

Ita mace bata duba da yanayin cewar ya mijin yake gwagwarmayar samowa shi kuma ba zai yi hakuri da tsusasa mata idan babu da yadda za ta yi kokari ta yi musu dabara ba.

Mafiya yawa mata suna hakuri da mazaje, maza abu ya hade musu biyu ga ko karancin samun aiki ko karancin jari ko karancin samun ubangida to maimakon idan ya zo ya nemi hadin kan matarsa matukar matar ta samu tarbiyya mai hankali ce  zaki ga ta yi kokari taga wane abune za ta bi wanda za ta fitar da mijinta daga wannan halin da yake ciki  to sai kiga an kasa samun wannan sai shi ya dau zafin kai ita kuma tana ganin ta ci wuya don abinda ke hannun ta duk yabi ya kare to inba a yi sa’a ba ta wannan bangaren sai kiga an samu mutuwar aure ta hanyar tambayar sa  abinda bashi dashi sai kiga nan da nan ya dau zafi sai ya yi sakin aure, domin shi sakin aure baya hannun mace, maza su ke sakin aure kuma basa duba da yadda Allah Ta’ala ya ce suyi rikon mataye cewa,”Fa’ansuku hunna bima’arufin Aufariƙuhunna bi maaruf’ Sadakallahul Azeem (ku rike matayenku da abin da shari’a ta gindaya muku), a’a su kuma basa duba  da abin da shari’a ta ce.

To a ganki wane ne yafi laifi matan ne ko mazan?

To gaskiya ni nafi ganin laifin mazan domin igiyar auren a hannunsu take kuma an riga an san cewa ita mace dole ne sai an yi hakuri da ita, domin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya nuna mana cewar ita mace hakarkarice wanda yake a tankware a jikin mutum idan ka yi kokarin matseta ka ce zaka mikar da ita tofa sai dai ta karye amma in kayi hakuri  zaka ji dadin a tankwaren ba’a samunta dari bisa dari haka Allah ya yi mu don ya baiwa mazaje kuuwarsu ‘Arrijali kauwamuna alal Nisa’ don Allah ya fito da wannan darajar tasu. To kinga ba za a ce laifin mace ne don an yi saki ba. Da ace ana bin dokokin da Allah ya shimfida da  aure bai mutu ba domin yana da  tsari sai anbi tsarin kayi fada sai kayi gargadi sai abin yaki ne to shi ne sai  wani hukunci da za ka yi sai a dauko adalai bangare biyu a bauko a bangaren mata a dauko bangaren maza in dai sun nemi sulhu to Allah zai sanya gyara a tsakanin su amma ba a daukar wannan tsarin, sai kaga mutum ko dan yana da kudi ya riga ya gama rugurguza yarinyar don maman ya saki ya dukunkule sai kiga da ya hango  wata tana yi masa yanga sai yaje ya dumbuzota ya zo ya ci mutuncin ta gida wannan abune da yake lalata tarbiya sai kiga yara ‘yan shaye shaye ga sunan da yawan su wadanda iyayen su basa a gida ne. Amma da mazan za su yi hakuri su ci gaba da tattalin ta gidan ana gyara mace ta dawo ta yi gargar amma sai kiga ya sa mata tsana da hantara wata ma kiga ta samu matsala hankalin ta ya gushe saboda bakan ta mata da musguna mata da ya keyi. Bayan da kadauketa mutum ka dauke ta mai daraja ce mai mutumci ce maimakon in zaka karo wata ita ka sanyaya mata rai a a sai kiga ya baza mata  da yawa malam bahaushe yana sakin matar sane in yazo aukar wata shi ne ake samun wadannan matsalolin amma idan aka yi wani duba ga wasu matan su suke jawa kansu matsala sai kiga mace daga haihuwa daya ko biyu ta maida kanta kazama kucaka tasaki ko ina tana shara ta saki Mama kasa yana lilo to taya zaka gano darajar ta amma takame kanta ta gyalgyale kanta ta ware yara gefe lokacin dawo warka ta taho tana yi maka Oyoyo dole ne zaka dinga samun farin ciki wannan kadanne daga cikin matsalolin mutuwar aure.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaAureMace-Macen AureMalamaMataMaza
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sakon Sabuwar Shekara: Na Yi Iya Bakin Kokarina Wajen Yi Wa Nijeriya Hidima A Mulkina — Buhari

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Tunbuke Kwamishinan Addinai Kan Rashin Mata Biyayya

Related

‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro
Taskira

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

2 months ago
Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan
Taskira

Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan

2 months ago
Me Ke Kawo Saurin Talaucewa Bayan Kammala Aikin Gwamnati?
Taskira

Me Ke Kawo Saurin Talaucewa Bayan Kammala Aikin Gwamnati?

3 months ago
Maganin Zubewar Mama Da Yadda Ake Gyara Shi 
Taskira

Yadda Mata Ke Daukar Yara Don Taya Su Aikin Gida

5 months ago
Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?
Taskira

Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?

8 months ago
Me Ya Fi Ci Wa Samari Da ‘Yan Mata Tuwo A Kwarya Game Da ‘Ramadan Basket’?
Taskira

Me Ya Fi Ci Wa Samari Da ‘Yan Mata Tuwo A Kwarya Game Da ‘Ramadan Basket’?

1 year ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Tunbuke Kwamishinan Addinai Kan Rashin Mata Biyayya

Gwamnatin Kano Ta Tunbuke Kwamishinan Addinai Kan Rashin Mata Biyayya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.