• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Fadadar Hadin Gwiwar BRICS Ke Alamtawa? 

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Fadadar Hadin Gwiwar BRICS Ke Alamtawa? 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon shekarar nan ta 2025, hadin gwiwar kungiyar BRICS ya samu wani sabon tagomashi. Inda a ranar 1 ga watan Janairun nan, a hukumance aka ayyana kasashen Kazakhstan, da Malaysia, da Cuba, da Bolivia, da Uganda a matsayin kasashe abokan tafiyar BRICS, kana a ranar 6 ga watan aka amince da kasar Indonesia a matsayin cikakkiyar mambar kawance na BRICS, mai kasashen Brazil, da Rasha, da Indonisiya, da Sin da Afirka ta Kudu.

Sabbin kare-karen dai sun bude wani sabon babi na bunkasa hadin gwiwar BRICS, wanda zai haifar da moriyar bai daya ta kasashe masu tasowa da masu saurin samun bunkasa. Ko shakka babu, fadadar hadin gwiwar BRICS zai samar da gudummawa ga dunkulewar tattalin arzikin duniya, da kyautata jagorancin sassan kasa da kasa, da zaman lafiya da ci gaban duniya.

  • Tattalin Arziki: Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Iya Ci Gaba Da Taimakawa Gwamnatin Tinubu Ba – Sarki Sanusi II
  • Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

Bana shekaru kusan 20 ke nan da kafuwar BRICS. Kuma a yau, kasashe mambobinta na da kusan rabin jimillar al’ummun duniya, da kaso sama da 30 bisa dari na daukacin GDPn duniya, suna kuma samar da gudummawar sama da kaso 50 bisa dari na tattalin arzikin duniya. Wanda hakan ke nuni ga yadda kungiyar ta zama wani ginshiki na daidaita harkokin kasa da kasa. Tabbas ci gaba da fadadar BRICS, alama ce mai nuni ga kyakkyawan tasirin hadin gwiwar da hadakar ke wanzarwa.

Gudummawar Sin ga hadin gwiwar BRICS

A matsayin kasa mai ingiza hadin gwiwar BRICS, har kullum kasar Sin na nacewa ga zurfafa matakan da za su kai ga bunkasa kungiyar, da yayata goyon baya, da farfadowar kasashe masu tasowa da masu saurin samun ci gaba. Mun ga yadda kasar Sin ta sanar da aniyarta, ta tsarin da zai sanya BRICS ta taka karin rawar gani a fannonin wanzar da zaman lafiya, da kirkire-kirkire, da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da tabbatar da adalci, da musayar kut da kut tsakanin al’ummun sassa daban daban na duniya, tare da kira ga kasashen BRICS da su yi hadin kai wajen tsare juna, da kafa tushen ci gaba mai inganci, da ingiza ci gaba mai dorewa, matakin da masharhanta da dama ke ganin ya kyautu ya zamo abun koyi ga sauran kasashen duniya masu fada a ji, da masu karfin tattalin arziki. (Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Fatan Kiyaye Duniyar Da Bil’adama Ke Rayuwa Da Samun Ci Gaba Mara Gurbata Muhalli

Next Post

Sabuwar Hanyar Kasuwancin Sin Ta Sada Tasoshin Jiragen Ruwa 555 A Duniya

Related

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya
Daga Birnin Sin

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

36 minutes ago
Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin
Daga Birnin Sin

Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

2 hours ago
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

3 hours ago
Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani
Daga Birnin Sin

Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

23 hours ago
Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka
Daga Birnin Sin

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

24 hours ago
Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban
Daga Birnin Sin

Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

24 hours ago
Next Post
Sabuwar Hanyar Kasuwancin Sin Ta Sada Tasoshin Jiragen Ruwa 555 A Duniya

Sabuwar Hanyar Kasuwancin Sin Ta Sada Tasoshin Jiragen Ruwa 555 A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

May 22, 2025
Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

May 22, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

May 22, 2025
Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

May 22, 2025
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

May 22, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

May 22, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

INEC Ta Samar Da Sashen Ƙirƙirarriyar Basira Domin Inganta Harkokin Zaɓe 

May 22, 2025
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

May 22, 2025
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

May 22, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.5 Don Magance Matsalar Abinci — Minista

Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.5 Don Magance Matsalar Abinci — Minista

May 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.