• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Haifar Da Koma Bayan Ababen More Rayuwa A Kasar Amurka?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Haifar Da Koma Bayan Ababen More Rayuwa A Kasar Amurka?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“A baya mun kasance na farko a duniya ta fannin ci gaban manyan ababen more rayuwa, amma yanzu an jera mu a matsayi na 14”, shugaban kasar Amurka Joe Biden ya bayyana damuwarsa game da yanayin da kasarsa ke ciki ta fannin ababen more rayuwa a yayin da yake rangadi a jihar Maine da ke arewa maso gabashin kasar a kwanan baya, inda ya kara da cewa, “ban manta ba, kasar Sin ta kasance a matsayi na 17 ko 16 a baya, amma ga shi ta zamanto na biyu yanzu. Me ya faru? Abin bai dace ba.” 

A hakika, ba wannan ne karo na farko da shugaba Biden ya kwatanta kasarsa da kasar Sin ta fannin ababen more rayuwa ba. A jawabin da ya gabatar a jihar North Carolina a watan Afrilun bara, ya kuma kwatanta filayen jirgin sama na kasashen biyu, inda ya ce, “idan dai na rufe idonka a daddare, kuma na kai ka filin jirgi na O’Hare, sa’an nan na kai ka wani filin jirgi na kasar Sin…lallai ya yiwu za ka dauka filin jirgi na kasar Sin namu ne, sakamakon yadda ya kasance na zamani matuka.”

  • Yunkurin Amurka Na Kakaba Takunkumi Kan Kamfanonin Sin Na Da Nufin Dakile Ci Gaban Jihar Xinjiang

Abin da ya fada haka yake, kasancewar Amurka kasa mafi karfin tattalin arziki a duniya, amma ababen more rayuwa na kasar sun tsufa har wasu sun lalace, wadanda ba su cancanci matsayin kasar ta fannin tattalin arziki ba. Idan ba a manta ba, a watan Faburairun wannan shekara, wani jirgin kasa da ke dauke da sinadarai masu guba ya kauce daga layin dogo a jihar Ohio ta kasar Amurka, lamarin da ya haifar da matsalar gurbacewar muhallin wurin. Abin bakin ciki shi ne, irin haduran ba su lissaftuwa a kasar ta Amurka. Alkaluman da hukumar kididdigar harkokin zirga-zirga ta kasar Amurka ta samar sun shaida cewa, daga shekarar 1990 zuwa ta 2021, gaba daya an samu hadura 54539 na kaucewar jiragen kasa daga layukan dogo, wato kimanin 1704 a kowace shekara.

Hakan ya sa wani mai bibbiyar shafukan yanar gizo ya saka wani hoto na kwatanta ababen more rayuwa na kasar Sin da Amurka, wanda ya kuma rubuta cewa, Amurka na zuba makudan kudade a fannin aikin soja a kowace shekara, a yayin da kuma kasar Sin ke zuba kudin a fannin gina ababen more rayuwa. Akwai kuma wani da ya rubuta cewa, “kasafin kudi a fannin aikin soja ya kai dalar Amurka biliyan 820, gwamnati ta kuma kebe wa yakin Ukraine dala biliyan 100, amma da an ce muna bukatar kudin gina ababen more rayuwa a gida, to, za ka ji ’yan siyasa sun ce daga ina za a samu kudin?”

A hakika, kalaman sun tona mana wani babban dalilin da ya sa ake samun koma bayan ababen more rayuwa a kasar Amurka, wato sabo da an zuba jari ga yaki a maimakon aikin gine-gine a cikin gida.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Kasancewar Amurka kasar da ke da tarihi na tsawon shekaru sama da 240 kawai, amma yake-yaken da ta tada ko kuma ta sa hannunta sun kai har sama da 200. Sanin kowa ne yake-yake na kashe makudan kudade, don haka, gwamnatin kasar Amurka ta zuba tarin kudi a yake-yake. Alkaluman da cibiyar SIPRI mai nazarin zaman lafiyar duniya da ke birnin Stockholm ta samar a watan Afrilun bana sun shaida cewa, kasar Amurka ce ta fi yawan zuba kudade ta fannin aikin soja a duniya, wadda a shekarar 2022 kadai, kudin da ta zuba a fannin ya kai dalar Amurka biliyan 877, wanda har ya dau kaso 39% na kudin soja da kasashen duniya suka zuba baki daya.

Kasar Sin a nata bangaren, tana ganin cewa, tabbatar da ci gaban kasa shi ne tushen daidaita dukkan matsalolin da ake fuskanta. Don haka ma, gwamnatin kasar ta dora matukar muhimmanci a kan gina ababen more rayuwa da saukaka fatara da ba da ilmi da kiwon lafiya da dai sauran muhimman fannonin da ke tabbatar da ci gaban kasa, tare kuma da cimma gaggaruman nasarori. Ban da raya kanta, kasar Sin ta kuma gabatar da shawarar raya kasashen duniya, inda ta yi kokarin aiwatar da hadin gwiwa da kasashen duniya, don fatan ganin tabbatar da ci gaban kasa da kasa, musamman ma kasashe masu tasowa. In mun dauki misali da Afirka, bisa tsarin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da na shawarar “ziri daya da hanya daya”, kasashen Afirka sun gane ma idanunsu manyan sauye-sauyen da suka faru gare su ta fannin ababen more rayuwa. Kawo yanzu, layin dogo da aka gina a kasashen Afirka bisa hadin gwiwar sassan biyu ya wuce kilomita dubu 10, baya ga hanyoyin mota da tsayinsu ya kai kusan kilomita dubu 100 da kuma gadoji kusan 1000 da tashoshin jiragen ruwa kusan 100, wadanda suka haifar da alfanu ga al’ummar kasashen.

Shugaba Biden na damuwa da koma bayan ababen more rayuwa a kasarsa, amma me ya haifar da hakan? Ya kamata ya yi tunani a kai. (Lubabatu Lei)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yunkurin Amurka Na Kakaba Takunkumi Kan Kamfanonin Sin Na Da Nufin Dakile Ci Gaban Jihar Xinjiang

Next Post

Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Zamfara Ta Amince Da Raba Kayan Abinci Don Tallafawa

Related

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

16 hours ago
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

18 hours ago
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

18 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

20 hours ago
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

20 hours ago
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

22 hours ago
Next Post
Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Zamfara Ta Amince Da Raba Kayan Abinci Don Tallafawa

Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Zamfara Ta Amince Da Raba Kayan Abinci Don Tallafawa

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A 16/05/2025

GORON JUMA’A 16/05/2025

May 16, 2025
Zargin Cin Zarafi: Gaskiyar Halin Da Ake Ciki A Gidan Yarin Goron Dutse

Zargin Cin Zarafi: Gaskiyar Halin Da Ake Ciki A Gidan Yarin Goron Dutse

May 16, 2025
Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista

Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista

May 16, 2025
Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

May 16, 2025
Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

May 16, 2025
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

May 16, 2025
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

May 16, 2025
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

May 16, 2025
Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.