• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Dangantaka Da Sin Ke Samun Karbuwa A Afrika?

byCGTN Hausa
2 years ago
Sin

Baki sama da 300 daga Sin da kasashen Afrika 53 ne suka tattauna a jiya Litinin game da gudanar da taron dandalin FOCAC na badi.  

Dandalin FOCAC dai ya kasance muhimmiyar laima da kasashen Sin da Afrika ke hadin gwiwa karkashinta, wanda kuma ke samun karbuwa matuka tsakanin kasashen Afrika. Shin me ya sa dangantaka da Sin ke kara samun karbuwa a Afrika?

  • Sin Na Fatan Za’a Daidaita Batun Palestinu Daga Dukkan Fannoni Kuma Na Dogon Lokaci
  • Bikin Ranar Majalisar Dinkin Duniya: Muna Fuskantar Kalubalen Da Ba A Taba Ganin Irinsa Ba – Schmale

Saboda kasar Sin ta zo da sabuwar dabarar hadin gwiwa da ba a saba gani ba. Wato mutuntawa da girmawawa da moriyar juna. A baya, hadin gwiwa da kasashen Afrika ke yi da iyayen gidansu, ta kasnace bisa wasu sharudda da wadancan kasashe ke gindayawa ko kuma ci da gumin kasashen da kwashe albarkatunsu. Amma a yanzu, ba haka abun yake ba, kasashen Afrika sun san darajar kansu saboda yadda kasar Sin ke daukarsu a matsayin ’yan uwanta ba tare da nuna iko ko fifiko ba.

Abu na biyu shi ne, kasar Sin tana fada da cikawa. Wato tana samar da tarin damarmaki tare da cika alkawuranta. Na yi imanin cewa, irin alfanun da kasashen suka samu daga hadin gwiwarsu da Sin a kankanin lokaci, bai kai abun da suka samu daga iyayen gidansu masu mulkin mallaka ba. Babu inda kasar Sin ba ta taba ba a fannonin rayuwar al’umma, kama daga ababen more rayuwa zuwa tsaro da kasuwanci da fasahohi da sauransu. Ba za a iya taba raba ci gaban da kasashen Afrika suka samu cikin sauri ba da taimakon kasar Sin.

Abu na 3 a ganina shi ne, yadda kasar Sin ta samarwa kasashen Afrika damar bayyana ra’ayinsu. Bisa yadda take tafiyar da dangantakarta da su, yanzu kasashen Afrika sun san abun da ya dace da su, da yadda za su kwaci kansu. Yayin wani taro da aka gudanar tsakanin kasashen Afrika da na Turai a kwanakin baya, na ji shugaban wata kasa a Afrika na cewa, lallai ya kamata a rika daukarsu da muhimmanci. Kuma kamata ya yi a rika ba su dama kamar sauran manyan kasashe. Wannan tamkar nanata kira da kokarin da kasar Sin ne na ganin duniya ba ta kasance karkashin ikon wata kasa ko wasu tsiraru ba.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Hakika kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen wayar da kai da ci gaban kasashen Afrika.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Gasar Wasannin Asiya Ajin Masu Bukata Ta Musaman Ta Hangzhou Ta Bayyana Kulawar Da Sin Take Baiwa Wannan Rukuni Na Al’umma

Gasar Wasannin Asiya Ajin Masu Bukata Ta Musaman Ta Hangzhou Ta Bayyana Kulawar Da Sin Take Baiwa Wannan Rukuni Na Al’umma

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version