• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kano Pillars Ta Fada Ajin Gajiyayyu A Nijeriya?

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Me Ya Sa Kano Pillars Ta Fada Ajin Gajiyayyu A Nijeriya?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Lahadin da ta gabata ne kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta tabbata cewa ta fadi daga gasar Firimiyar Nijeriya bana duk da nasarar da ta samu a wasanta na karshe akan Shooting Stars da ci 2-1 a filin wasa na Sani Abacha dake Kofar Mata a nan Kano.

Wannan dai shi ne karo na uku da kungiyar ta fada ajin gajiyayyu a tarihi tun bayan kafa ta a shekarar 1990, Pillars dai ta taba faduwa daga gasar Firimiya a shekarar 1994 da 1999, sai kuma wannan karon.

  • ‘Yan Sandan Birnin Milan Sun Ba Wa Dan Wasa Bukayoko Hakuri

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars dai ta taba lashe gasar firimiyar Nigeriya sau hudu inda ta lashe a shekarar 2008 da 2012 da 2013 sai kuma kakar wasa ta 2014, sannan a shekarar 2019 ta lashe gasar Aito Cup.

Kano Pillars tana da tarihi a fagen kwallon kafa a Nigeriya da kuma nahiyar Afirka, inda ko a shekarar 2009 sai da kungiyar ta samu damar zuwa wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin nahiyar Afirka.

Sai dai me ya sa Pillars din ta fada ajin gajiyayyu?
Rashin Kwararren Shugaba
Mutane da dama dai suna ganin shugaban kungiyar, Surajo Yahaya Jambul, wanda aka dakatar, bashi da cikakkiyar kwarewar da zai iya jan ragamar kungiyar hart a samu irin ci gaban da ake bukata musamman saboda rashin kwarewarsa akan harkokin wasanni.

Labarai Masu Nasaba

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Unity Cup: Yau Nijeriya Da Ghana Zasu Kece Raini A Birnin Landan

A shekara ta 2019 ne gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya nada Surajo Shu’aibu Yahaya da ake kira Jambul a matsayin shugaban kungiyar ta Kano Pillars sai dai tun bayan da aka nada shi shugabanci wasu suka fara korafin cewar bai da kwarewar jan ragamar babbar kungiya kamar Pillars.

Magoya bayan kungiyar dai na ganin bai kamata tun farko a sauya tsohon shugaban kungiyar ba, Alhaji Tukur Babangida, wanda ya goge a sanin kwallon kafar kasar nan da kuma shige-shigen da ake yi a harkar.

Surajo Jambul ya karbi shugabancin kungiyar a lokacin da kungiyar take dab da daukar gasar cin kofin kalubale ta Aiteo Cup sannan kuma kungiyar ta yi ta biyu a kakar da aka kammala a lokacin.
Amma sai dai a kakar ya ja ragamar kungiyar ta yi ban kwana da gasar kofin Zakarun Afirka wato Champions League, inda Ashanti Kotoko ta Ghana ta yi nasara a kan Pillars 5-2 gida da waje sannan a kakar gaba aka yi waje da Pillars a gasar Confederation Cup, kuma wata karamar kungiya ta Senegal mai suna Jaraaf, wadda ta ci Pillars din 3-1 gida da waje.

Sannan bayan kasa taka rawar gani a wasannin zakarun Afirka, Kano Pillars ta ci gaba da rashin kokari a wasannin da take buga wa a Firimiya wanda magoya bayan kungiyar tun a wancan lokacin suka dinga kiraye-kiraye akan a kawo canji.

Bugu da kari, wasu suna ganin gwamnatin Jihar Kano ta janye daga bai wa Kano Pillars kudi kamar yadda aka saba yi, in banda albashin ‘yan wasa wanda hakan ya sa ‘yan wasa suka koma ba sa samun ladan wasa da sauran kudaden da suke kara karsashin ‘yan kwallo domin suke saka kwazo.

Amma wasu sun ce gwamnatin ko ta bayar da kudi kwalliya ba ta biyan kudin sabulu, saboda rashin kwarewar shugabanci wanda yana daya daga cikin abin da aka zargi kungiyar da shi tun farkon fara wannan kakar.

Rashin Buga Wasannin Gida A Kano
Kano Pillars ta koma buga wasanninta na gida a Jihar Kaduna, filin da ake kira Ahmadu Bello daga nan ta koma Jihar Katsina, filin wasa na Muhammadu Dikko sannan kuma daga nan ta koma wasa a Kano nan da nan kungiyar ta yi laifin da aka dauke ta zuwa Abuja, filin MKO Abiola na babban birnin tarayya, har ila yau daga nan kuma Pillars ta sake komawa buga wasanninta na gida a Sani Abacha da ke kofar mata, a Kano.

A dai kakar bana da Pillars ke fatan hada maki sai kungiyar ta ci karo da koma bayan da aka ci gaba da zargin Jambul da rashin iya gudanar da mulki sannan matsi ya ci gaba da hawan shugaban, wanda magoya baya suke ta shakkun da kyar idan kungiyar ba ta yi abin kunya ba.

Kwashe wa kungiyar Maki Shida
Tun bayan da Kano Pillars ta koma Kano buga wasa wato filin wasa na Sani Abacha, an samu yamutsin fasa motar Katsina United cikin watan Afirilu sannan an kara kwashe mata maki uku daga Kano Pillars kan laifin da Jambul ya aikata a karawa da kungiyar Dakkada.

Hukumar gudanar da gasar Firimiya ta kasa, LMC ta dakatar da shugaban Kano Pillars, Suraj Yahaya daga shiga harkokin wasanninta nan take bayan da aka tuhumi Kano Pillars da karya doka ta gudanar da wasannin Firimiya a lokacin da ta buga karawa da Dakkada ranar 23 ga watan Yunin 2022.

Halayyar magoya baya
Kungiyar magoya bayan Kano Pillars mai dunbin magoya baya itama ta bayar da gudunmawa wajen faduwar kungiyar daga gasar Firimiya a bana saboda yadda magoya bayan suka kasa nuna halin da’a a wasannin da ta buga a Kaduna da Katsina, wanda hukumar gudanar da gasar ta Nijeriya ke ta gargadinsu.

Maganar rikici da tayar da yamutsi ba abin da yake kawo ci gaba ba ne a kungiyar, amma magoya bayan Pillars sun yi suna a rashin hakuri a lokacin buga wasa kuma za’a iya cewa a yanzu wannan halayya ta jawo wa kungiyar koma baya.

Sannan ana ganin cewar Kano Pillars ba ta dauki ‘yan wasan da suka da ce ba musamman a kakar nan, idan ba haka ba ya kamata su fahimci cewar sana’arsu ce ba wanda zai kama musu sai dai kwazonsu.

Amma kuma rashin samun kudi a kan kari ya taka rawar gani da ‘yan kwallon suka kasa sa kwazo a wasanninsu, ga tarin matsaloli sannan bayan da abubuwa suka yi lalacewar da ba damar gyara, shi ne aka kori Surajo Shu’aibu Yahaya aka nada Alhaji Ibrahim Galadima na rikon kwarya.

Kungiyar Kano Pillars ta karkare a mataki na 19 da maki 45, bayan da ta ci wasa tara da canjaras tara aka doke ta karawa 20.

Haka kuma an zura kwallo 50 a ragar Pillars, ita kuma ta ci 26 a kakar bana da hakan ya sa ta yi ban kwana da babbar gasar ta Nijeriya da aka karkare amma sai dai kuma wasu na cewar watakila Kano Pillars ta buga gasar nan gaba, bayan da kungiyar Gombe mai suna Doma United ta samu gurbin shiga gasar kaka mai zuwa, amma wasu na cewar za ta sayar da gurbin ne.

An ce kungiyar ta Gombe na neman Naira miliyan 250 daga Kano Pillars, sai su yi musaya, masu gida ta koma Firimiya ita kuwa Doma ta ci gaba da buga rukuni na biyu kuma ba wannan karon bane ake cinikin gurbi a gasar firimiyar ta Nijeriya, domin Kwara United ta yi haka a shekarar 2019, haka itama Delta ta sayi gurbi a wajen Kada City.

Saboda haka wasu na ganin ya kamata a kawo sayen gurbi tsakanin kungiyoyi idan har ana son gasar ta yi armashi kuma yakamata a kafa dokar da za ta samar da fitattun kungiyoyin da za su ke wakiltar kasar a wasannin waje domin kai wa gurbin da ya kamata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Nijeriya Idan Ka Ce Za Ka Rike Aikin Gwamnati Shi Kadai Akwai Kalubale – Fatima (Adon Gari)

Next Post

Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Sun Roki Manyan Kasashen Duniya Su Kawo Musu Dauki 

Related

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo
Wasanni

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

5 hours ago
Unity Cup: Yau Nijeriya Da Ghana Zasu Kece Raini A Birnin Landan
Wasanni

Unity Cup: Yau Nijeriya Da Ghana Zasu Kece Raini A Birnin Landan

2 days ago
Yamal Ya Saka Hannu A Sabon Kwantiragin Shekaru 6 A Barcelona 
Wasanni

Yamal Ya Saka Hannu A Sabon Kwantiragin Shekaru 6 A Barcelona 

2 days ago
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila
Wasanni

Ina Fatan Cigaba Da Taka Leda Har Zuwa Lokacin da Zan Cika Shekara 40 A Duniya – Salah

2 days ago
Kofin Duniya
Wasanni

Kofin Duniya: Kasar Saudiyya Za Ta Sassauta Dokar Hana Shan Giya A Wuraren Yawon Bude Ido 600

3 days ago
Chelsea, Man City, Newcastle Sun Samu Gurbi A Gasar Zakarun Turai Ta Baɗi
Wasanni

Chelsea, Man City, Newcastle Sun Samu Gurbi A Gasar Zakarun Turai Ta Baɗi

4 days ago
Next Post
Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Sun Roki Manyan Kasashen Duniya Su Kawo Musu Dauki 

Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Sun Roki Manyan Kasashen Duniya Su Kawo Musu Dauki 

LABARAI MASU NASABA

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

May 29, 2025
An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

May 29, 2025
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

May 29, 2025
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

May 29, 2025
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

May 29, 2025
Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

May 29, 2025
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

May 29, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

May 29, 2025
AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

May 29, 2025
Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

May 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.