• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Yake Faruwa Da Kungiyar Brighton A Kakar Bana?

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
in Wasanni
0
Me Yake Faruwa Da Kungiyar Brighton A Kakar Bana?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana harkar kwallon kafa sun bayyana cewar da wuya Brighton ta iya taka rawar gani kwatankwacin wanda ta yi a kakar da ta gabata. Shekarar da ta gabata kungiyar kwallon kafa ta Brighton And Hobe Albion, ta nuna wa duniya cewar ita ba kanwar lasa bace a harkar kwallon kafa inda ta dinga lallasa wasu daga cikin manyan kungiyoyin kwallon kafa dake buga gasar Firimiya da suka hada da Manchester United da kuma Chelsea.

Ta ci gaba da taka rawar gani da har ya sa ta samu gurbin buga gasar Uefa Europa League a karon farko a tarihinta bayan ta kammala kakar bara a mataki na 6.

  • Manchester United Zata Sayar Da Kashi 25 Na Kungiyar Akan Yuro Biliyan 1.3
  • Newcastle Ta Dauki Harvey Barnes Daga Leicester City

Amma kamar zancen ya canza a bana domin kuwa a daidai wannan lokacin a bara Brighton tana mataki na uku, ba kamar bana da take ta 6 a teburin Firimiya ba bayan wasanni 8. Sannan kuma a gasar UEFA Europa League, Brighton tana zaune a karshen rukunin B bayan rashin nasara daya da canjaras daya.

Ba abin mamaki bane ganin cewar Brighton ta rabu da manyan ‘yan was anta da suka hada da Moses Caicedo da Mac Allister a kan kudade masu dimbin yawa. Wanda masu sharhi kan harkokin wasan kwallon kafa ke gani a matsayin wani babban dalilin da zai iya hana kungiyar tabuka wani abin a zo a gani a bana.

Kocin kungiyar De Zerbi yayin wata hira da ya yi da yan jarida ya bayyana cewar yana da matukar kwarin gwiwa akan ‘yan wasansa, kuma yana da yakinin cewar za su iya kai kungiyar inda ake da bukata.

Labarai Masu Nasaba

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

De Zerbi ya karbi aikin horar da Brighton a bara bayan tashin tsohon kocinsu Graham Potter wanda ya koma Chelsea a kakar bara. Tun daga lokaci De Zerbi ya nuna kwarewarsa a harkar horarwa bayan jagorantar Brighton zuwa buga gasar UEFA Europa League.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Manchester UnitedPremier leagueUEFA
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Baje Kolin Canton Karo Na 134 A Guangzhou

Next Post

CMG Da Kafofin Watsa Labaran Afirka Sun Fitar Da Shawarar Aiki Kan Ziri Daya Da Hanya Daya

Related

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

22 hours ago
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
Wasanni

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

1 day ago
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
Wasanni

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

2 days ago
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
Wasanni

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

4 days ago
Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 
Wasanni

Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

4 days ago
Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi
Wasanni

Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi

5 days ago
Next Post
CMG Da Kafofin Watsa Labaran Afirka Sun Fitar Da Shawarar Aiki Kan Ziri Daya Da Hanya Daya

CMG Da Kafofin Watsa Labaran Afirka Sun Fitar Da Shawarar Aiki Kan Ziri Daya Da Hanya Daya

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

June 26, 2025
Kawayen amarya

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.