• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Japan Ke Daukar Wasu Matakan Da Ka Iya Haifar Da Hadari?

by CGTN Hausa
2 years ago
Japan

A kwanan nan kasar Japan ta rika daukar wasu matakan da ka iya haifar da hadarin gaske, ciki har da kara karfafa yarjejeniyar tsaro tsakanin ta da Amurka a wasu manyan fannoni, da hada kai tare da kasashen Amurka, da Australiya, da Philippines, don gudanar da atisayen soja a tekun kudancin kasar Sin, da kuma neman shiga kungiyar AUKUS, al’amarin da ya sha suka sosai daga bangarori daban-daban.

Daga cikin dukkan wadannan abubuwa, abun da ya fi janyo ce-ce-ku-ce shi ne, karfafa kawancen soja tsakanin Amurka da Japan. A wajen taron kolin shugabannin Amurka da Japan da aka yi a birnin Washington a wannan karo, an samu wani gagarumin ci gaba da ba’a taba ganin irinsa ba a shekaru sama da 60 ga yarjejeniyar tsaro ta kasashen biyu, ciki har da yi wa rundunar sojan Amurka dake Japan garambawul, da kara hadin-kai ta fuskar soja, da nufin kawo sauye-sauye ga ayyukan rundunar tsaron gidan Japan, har ta zama “rundunar masu kai hari”, gami da kara dunkule kasashen Amurka da Japan ta fannin aikin soja.

  • Harin Sojoji A Kauyen Sudan Ya Kashe Mutum 28
  • Harin Sojoji A Kauyen Sudan Ya Kashe Mutum 28

Manazarta na ganin cewa, wadannan sabbin matakan da Japan ta aiwatar, sun shaida cewa, kasar na kara nisanta kanta daga kundin tsarin mulki na kiyaye zaman lafiya, da bada hadin-kai matuka ga manyan tsare-tsaren Amurka, domin kawo cikas ga ci gaban kasar Sin.

Kaza lika, matakan da Japan ta aiwatar sun ja hankulan bangarori daban-daban, inda jaridar “Asahi Shimbun” ta Japan ta ruwaito cewa, ana kara nuna shakku kan kimar Japan, a matsayin wata kasa dake son shimfida zaman lafiya.

A matsayinta na kasa mafi girma ta fuskar aikin soja a duniya, yunkurin Amurka na shiga cikin harkokin yankin Asiya da tekun Pasifik na tattare da dalilan soja. Kuma inganta kawancen soja tsakanin Amurka da Japan, ka iya kawo sauyi ga halin daidaito na yankin, da janyo damuwa, da rashin gamsuwa daga sauran kasashe, da yin barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankalin yankin. (Murtala Zhang)

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
Daga Birnin Sin

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
Daga Birnin Sin

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Next Post
Sanata yari

Shugaban Kasa ne Ke Iya Magance Matsalar Tsaro Ba Gwamnoni Ba - Sanata Yari

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.