• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Buƙaci Jihohi Su Sake Tunani Kan Duk Wani Yunƙurin Rushe Ma’aikatun Yaɗa Labarai

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Minista Ya Buƙaci Jihohi Su Sake Tunani Kan Duk Wani Yunƙurin Rushe Ma’aikatun Yaɗa Labarai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga gwamnatocin jihohi da ke tunanin rusawa ko rage matsayin Ma’aikatun yada Labarai da su sake tunani, yana mai jaddada mahimmancin su wajen hulɗa da jama’a, wayar da kai, da kuma haɗin kan al’umma.

 

Idris ya yi wannan kiran ne yayin taron Majalisar Ƙasa kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai karo na 48 a Kaduna a ranar Juma’a, mai taken “Inganta Gudanar da Yaɗa Labarai don Shugabanci Mai Haɗin Kai: Ajandar Sabunta Fata.”

  • ASUU Reshen Jami’ar Sa’adu Zungur Ta Dakatar Da Yajin Aiki
  • Rai Da Lafiyar Mazajenmu Ya Fi Mana Jarumtarsu

Ya ce, “A wannan lokaci, ina son yin roƙo mai matuƙar mahimmanci ga wasu daga cikin gwamnatocin jihohin mu, musamman kan matsayi da ayyukan Ma’aikatun Yaɗa Labarai na Jihohi.

 

Labarai Masu Nasaba

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

“Kuma roƙo na shi ne: a shugabanci, ba za a taɓa musanta muhimmancin Ma’aikatun Labarai ba a matakin tarayya da jiha. Waɗannan Ma’aikatu sun zama wata gada tsakanin manufofin gwamnati da ‘yan ƙasa da aka tsara su amfana da su, ta yadda za su samar da gaskiya, da riƙon amana, waɗanda su ne ginshiƙan kowace dimokiraɗiyya mai ci gaba.”

 

Idris ya jaddada cewa Ma’aikatun Yaɗa Labarai suna da matuƙar muhimmanci wajen wayar da kan jama’a, yaƙi da labaran ƙarya, da tabbatar da isar da manufofi da shirye-shiryen gwamnati yadda ya kamata.

 

Ya bayyana ma’aikatar a matsayin “jigon dimokiraɗiyya da cigaba,” musamman a ƙasa mai ɗimbin bambance-bambance kamar Nijeriya.

 

Da yake magana akan Ajandar Sabunta Fata na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Idris ya ce wannan kira ne na shugabanci mai kawo sauyi wanda ya dogara kan haɗin kai da gaskiya.

 

Ya ce shugabanci ya ta’allaƙa ne ga iyawarsa na haɗawa, sadarwa, da ƙarfafa haɗin gwiwar jama’a.

 

Ministan ya shawarci Manajojin Watsa Labarai da su yi amfani da fasaha, ciki har da na’ura mai ƙwaƙwalwa (AI), don inganta sauri da sahihancin saƙonnin su.

 

Ya kuma jaddada muhimmancin muhawarar jama’a wajen gyaran manufofi, yana bada misali da tattaunawar da ake yi kan sauye-sauyen haraji da Shugaba Tinubu ya gabatar.

 

“A kowace dimokuraɗiyya, karfin shugabanci yana da tushe sosai a cikin ikonsa na nuna muradun jama’a. Manufofin jama’a, yayin da aka ƙera su da kyakkyawar niyya, dole ne su ci gaba da bunƙasa don biyan buƙatu da tsammanin ‘yan ƙasa,” inji Idris.

 

Idris ya kuma jaddada buƙatar horas da jami’an yaɗa labarai kan dabarun tabbatar da gaskiya da haɓaka haɗin gwiwa da kafofin watsa labarai don yaƙi da labaran ƙarya.

 

Ya bayyana cewa Shugaba Tinubu kwanan nan ya amince da sakin kuɗi don fara aiki da Cibiyar UNESCO ta Category-2 Media and Information Literacy (MIL), wacce za a kafa a Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya (NOUN) da ke Abuja.

 

Ya ce, “A lokacin da labaran ƙarya, furofaganda, da rahotannin son zuciya ke iya tasiri sosai kan ra’ayin jama’a da yanke shawara, fahimtar kafofin watsa labarai yana ƙarfafa tunani mai zurfi.

 

“Yana taimaka wa mutane su nazarci manufar saƙonnin kafofin watsa labarai, su fahimci yanayin da aka gabatar da su, da kuma tantance sahihancin su.

 

“Don haka ina kira ga Kwamishinonin Yaɗa Labarai da su yi amfani da wannan cibiya mai matuƙar muhimmanci da zarar ta fara aiki domin ƙara inganta ƙwarewar ma’aikatansu wajen yaƙar labaran ƙarya,” inji shi.

 

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, shi ne ya buɗe taron.

 

Taron ya samu halartar manyan masu ruwa da tsaki da suka haɗa da Sanata Kenneth Eze, Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, da Hon. Olusola Steve Fatoba, Shugaban Kwamitin Majalisar Wakilai kan Yaɗa Labarai, Wayar da Kai, Ɗa’a, da Ɗabi’u.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Ci Gaba Da Amfani Da Kaso Mai Yawa Na Lantarkin Makamashin Iska Da Hasken Rana

Next Post

Sin Ta Fitar Da Matakan Zamanantar Da Sana’ar Hada-Hadar Kayayyaki

Related

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
Labarai

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

7 minutes ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

2 hours ago
bakin wake
Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

4 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

6 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

8 hours ago
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Labarai

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

8 hours ago
Next Post
Sin Ta Fitar Da Matakan Zamanantar Da Sana’ar Hada-Hadar Kayayyaki

Sin Ta Fitar Da Matakan Zamanantar Da Sana'ar Hada-Hadar Kayayyaki

LABARAI MASU NASABA

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.