• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Rungumi Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa

by Sulaiman
12 months ago
Amurka

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya (NPF) da ta rungumi Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa.

 

Ya bayyana cewa, rungumar ƙa’idojin Yarjejeniyar zai inganta kallo da fahimtar da jama’a suke yi wa rundunar.

  • Xi Ya Yi Kiran Gina Duniya Mai Ci Gaba Ta Bai Daya Bisa Adalci A Taron G20
  • An Fara Watsa Shirin Zababbun Kalaman Da Shugaba Xi Jinping Ya Fi Kauna A Kasar Brazil

Sanarwar da Mataimaki na Musamman ga Ministan kan Harkokin Yaɗa Labarai, Rabiu Ibrahim, ya fitar ta nuna cewa ministan ya bayyana hakan ne a yayin wani taron ƙara wa juna sani na jami’an hulɗa da jama’a na ‘yan sanda wanda aka yi a Asaba, Jihar Delta.

 

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

Idris, wanda ya samu wakilcin Darakta-Janar na gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON), Malam Jibrin Baba-Ndace, ya ce: “An ƙirƙiri Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa a matsayin tsarin ayyana mu a matsayin ’yan Nijeriya da kuma tabbatar da manufofin mu na gaskiya a cikin muradin mu.

 

“Tana cike giɓin da aka samu wajen neman haɗin kan ƙasa, cigaban al’umma, da kishin ƙasa mai ɗorewa a tsakanin ‘yan Nijeriya.

 

“Don haka ina amfani da wannan dama don yin kira ga Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya da ta rungumi yarjejeniyar ɗa’ar da zuciya ɗaya, tare da yin amfani da ita don ƙirƙirar sabon labari na Nijeriya.

 

“Dole ne dukkan mu mu gane cewa ‘Yan Sandan Nijeriya na kan gaba wajen yadda ake kallon ƙasar mu a cikin ƙasa da kuma duniya.”

 

Ministan ya bayyana irin rawar da ‘yan sanda ke takawa a matsayin hukumar tsaro ta farko da ke mu’amala da al’ummar Nijeriya.

 

Ya yi nuni da cewa aikin rundunar ya wuce tabbatar da bin doka da oda, ya kai ga kare rayuka, mutunci, ‘yanci, da dukiyoyin ‘yan ƙasa, inda ya jaddada muhimmancin yin aiki da kundin tsarin mulki da kuma yarjejeniyar zamantakewa da ‘yan ƙasa.

 

Ya ƙara da cewa aikin ‘yan sanda mai inganci ya dogara ne da fahimtar juna da kuma wani nauyi da ya rataya a wuyan ‘yan sanda, gwamnati, da jama’a, yana mai cewa amanar jama’a ita ce ƙalubale mafi girma da rundunar take fuskanta a yau.

 

Ya ce: “A cigaban da muke samu a matsayin mu na ƙasa da kuma cigaban mutuncin mu, ‘yan sanda sun yi fafutuka wajen mu’amala da jama’a, musamman saboda saɓani na kare haƙƙin jama’a da tabbatar da zaman lafiya a ƙasar.

 

“Wannan gwagwarmaya ta ƙara zama ƙalubale saboda akwai wasu abubuwan cikin gida masu hani da ke dagula tasirin ƙwararrun ‘yan sanda wajen gudanar da ayyukan su.”

 

Ministan ya yaba wa shugabannin NPF da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, bisa shirya taron.

 

Ya kuma amince da daidaita ayyukan rundunar tare da manufar Shugaba Bola Tinubu ta samun ingantaccen aiki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama
Manyan Labarai

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Next Post
Bangaren Sin Ya Yi Kiran Tsagaita Bude Wuta A Sudan Cikin Hanzari

Bangaren Sin Ya Yi Kiran Tsagaita Bude Wuta A Sudan Cikin Hanzari

LABARAI MASU NASABA

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.