• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Rungumi Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa

by Sulaiman
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya (NPF) da ta rungumi Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa.

 

Ya bayyana cewa, rungumar ƙa’idojin Yarjejeniyar zai inganta kallo da fahimtar da jama’a suke yi wa rundunar.

  • Xi Ya Yi Kiran Gina Duniya Mai Ci Gaba Ta Bai Daya Bisa Adalci A Taron G20
  • An Fara Watsa Shirin Zababbun Kalaman Da Shugaba Xi Jinping Ya Fi Kauna A Kasar Brazil

Sanarwar da Mataimaki na Musamman ga Ministan kan Harkokin Yaɗa Labarai, Rabiu Ibrahim, ya fitar ta nuna cewa ministan ya bayyana hakan ne a yayin wani taron ƙara wa juna sani na jami’an hulɗa da jama’a na ‘yan sanda wanda aka yi a Asaba, Jihar Delta.

 

Labarai Masu Nasaba

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

Idris, wanda ya samu wakilcin Darakta-Janar na gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON), Malam Jibrin Baba-Ndace, ya ce: “An ƙirƙiri Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa a matsayin tsarin ayyana mu a matsayin ’yan Nijeriya da kuma tabbatar da manufofin mu na gaskiya a cikin muradin mu.

 

“Tana cike giɓin da aka samu wajen neman haɗin kan ƙasa, cigaban al’umma, da kishin ƙasa mai ɗorewa a tsakanin ‘yan Nijeriya.

 

“Don haka ina amfani da wannan dama don yin kira ga Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya da ta rungumi yarjejeniyar ɗa’ar da zuciya ɗaya, tare da yin amfani da ita don ƙirƙirar sabon labari na Nijeriya.

 

“Dole ne dukkan mu mu gane cewa ‘Yan Sandan Nijeriya na kan gaba wajen yadda ake kallon ƙasar mu a cikin ƙasa da kuma duniya.”

 

Ministan ya bayyana irin rawar da ‘yan sanda ke takawa a matsayin hukumar tsaro ta farko da ke mu’amala da al’ummar Nijeriya.

 

Ya yi nuni da cewa aikin rundunar ya wuce tabbatar da bin doka da oda, ya kai ga kare rayuka, mutunci, ‘yanci, da dukiyoyin ‘yan ƙasa, inda ya jaddada muhimmancin yin aiki da kundin tsarin mulki da kuma yarjejeniyar zamantakewa da ‘yan ƙasa.

 

Ya ƙara da cewa aikin ‘yan sanda mai inganci ya dogara ne da fahimtar juna da kuma wani nauyi da ya rataya a wuyan ‘yan sanda, gwamnati, da jama’a, yana mai cewa amanar jama’a ita ce ƙalubale mafi girma da rundunar take fuskanta a yau.

 

Ya ce: “A cigaban da muke samu a matsayin mu na ƙasa da kuma cigaban mutuncin mu, ‘yan sanda sun yi fafutuka wajen mu’amala da jama’a, musamman saboda saɓani na kare haƙƙin jama’a da tabbatar da zaman lafiya a ƙasar.

 

“Wannan gwagwarmaya ta ƙara zama ƙalubale saboda akwai wasu abubuwan cikin gida masu hani da ke dagula tasirin ƙwararrun ‘yan sanda wajen gudanar da ayyukan su.”

 

Ministan ya yaba wa shugabannin NPF da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, bisa shirya taron.

 

Ya kuma amince da daidaita ayyukan rundunar tare da manufar Shugaba Bola Tinubu ta samun ingantaccen aiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Yi Kiran Gina Duniya Mai Ci Gaba Ta Bai Daya Bisa Adalci A Taron G20

Next Post

Bangaren Sin Ya Yi Kiran Tsagaita Bude Wuta A Sudan Cikin Hanzari

Related

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

9 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

12 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

16 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

19 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

1 day ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

1 day ago
Next Post
Bangaren Sin Ya Yi Kiran Tsagaita Bude Wuta A Sudan Cikin Hanzari

Bangaren Sin Ya Yi Kiran Tsagaita Bude Wuta A Sudan Cikin Hanzari

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.