• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Rungumi Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa

by Sulaiman
11 months ago
Amurka

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya (NPF) da ta rungumi Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa.

 

Ya bayyana cewa, rungumar ƙa’idojin Yarjejeniyar zai inganta kallo da fahimtar da jama’a suke yi wa rundunar.

  • Xi Ya Yi Kiran Gina Duniya Mai Ci Gaba Ta Bai Daya Bisa Adalci A Taron G20
  • An Fara Watsa Shirin Zababbun Kalaman Da Shugaba Xi Jinping Ya Fi Kauna A Kasar Brazil

Sanarwar da Mataimaki na Musamman ga Ministan kan Harkokin Yaɗa Labarai, Rabiu Ibrahim, ya fitar ta nuna cewa ministan ya bayyana hakan ne a yayin wani taron ƙara wa juna sani na jami’an hulɗa da jama’a na ‘yan sanda wanda aka yi a Asaba, Jihar Delta.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

Idris, wanda ya samu wakilcin Darakta-Janar na gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON), Malam Jibrin Baba-Ndace, ya ce: “An ƙirƙiri Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa a matsayin tsarin ayyana mu a matsayin ’yan Nijeriya da kuma tabbatar da manufofin mu na gaskiya a cikin muradin mu.

 

“Tana cike giɓin da aka samu wajen neman haɗin kan ƙasa, cigaban al’umma, da kishin ƙasa mai ɗorewa a tsakanin ‘yan Nijeriya.

 

“Don haka ina amfani da wannan dama don yin kira ga Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya da ta rungumi yarjejeniyar ɗa’ar da zuciya ɗaya, tare da yin amfani da ita don ƙirƙirar sabon labari na Nijeriya.

 

“Dole ne dukkan mu mu gane cewa ‘Yan Sandan Nijeriya na kan gaba wajen yadda ake kallon ƙasar mu a cikin ƙasa da kuma duniya.”

 

Ministan ya bayyana irin rawar da ‘yan sanda ke takawa a matsayin hukumar tsaro ta farko da ke mu’amala da al’ummar Nijeriya.

 

Ya yi nuni da cewa aikin rundunar ya wuce tabbatar da bin doka da oda, ya kai ga kare rayuka, mutunci, ‘yanci, da dukiyoyin ‘yan ƙasa, inda ya jaddada muhimmancin yin aiki da kundin tsarin mulki da kuma yarjejeniyar zamantakewa da ‘yan ƙasa.

 

Ya ƙara da cewa aikin ‘yan sanda mai inganci ya dogara ne da fahimtar juna da kuma wani nauyi da ya rataya a wuyan ‘yan sanda, gwamnati, da jama’a, yana mai cewa amanar jama’a ita ce ƙalubale mafi girma da rundunar take fuskanta a yau.

 

Ya ce: “A cigaban da muke samu a matsayin mu na ƙasa da kuma cigaban mutuncin mu, ‘yan sanda sun yi fafutuka wajen mu’amala da jama’a, musamman saboda saɓani na kare haƙƙin jama’a da tabbatar da zaman lafiya a ƙasar.

 

“Wannan gwagwarmaya ta ƙara zama ƙalubale saboda akwai wasu abubuwan cikin gida masu hani da ke dagula tasirin ƙwararrun ‘yan sanda wajen gudanar da ayyukan su.”

 

Ministan ya yaba wa shugabannin NPF da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, bisa shirya taron.

 

Ya kuma amince da daidaita ayyukan rundunar tare da manufar Shugaba Bola Tinubu ta samun ingantaccen aiki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Minista
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Next Post
Bangaren Sin Ya Yi Kiran Tsagaita Bude Wuta A Sudan Cikin Hanzari

Bangaren Sin Ya Yi Kiran Tsagaita Bude Wuta A Sudan Cikin Hanzari

LABARAI MASU NASABA

Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Minista

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.