• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

MOFA: Batun Taiwan Ba Ya Bukatar Tsangwama Daga Waje

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
MOFA: Batun Taiwan Ba Ya Bukatar Tsangwama Daga Waje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya fada a wata hira da ya yi cewa, idan aka samu rikici na soji tsakanin bangarori biyu na mashigin tekun Taiwan, bai kawar da yiwuwar shiga tsakani na sojojin Amurka ba. Dangane da hakan, yayin da take mayar da martani, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana a gun taron manema labarai da aka saba gudanarwa a yau 5 ga wata cewa, Taiwan wani yanki ne da ba zai taba rabuwa da kasar Sin ba, kuma batun Taiwan lamari ne na cikin gida na kasar Sin wanda ba ya lamuntar tsoma baki daga waje.

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Sun Weidong zai jagoranci wata tawaga da za ta halarci taron manyan jami’an ASEAN da Sin da Japan da Koriya ta Kudu, da taron manyan jami’ai na gabashin Asiya, da taron manyan jami’ai na dandalin tattaunawar ASEAN da za a yi a Vientiane a ranar 7 zuwa 8 ga wata. Mao Ning ta kara da cewa, kasar Sin na fatan yin mu’amala mai zurfi tare da dukkan bangarorin da za su halarci tarukan, domin sa kaimi ga samun sabbin ci gaba a hadin gwiwar dake tsakanin kasashen gabashin Asiya, da ba da gudummawa sosai wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da samun ci gaba tare.

  • Sin Tana Son Yin Aiki Tare Da Hukumar IAEA Don Tabbatar Da Shawarar Ci Gaban Duniya Da Shawarar Tsaron Duniya
  • Wang Yi: Karin Kasashe Na Nuna Goyon Baya, Za A Kyautata Fatan Samun Zaman Lafiya

Ban da haka kuma, kasar Sin ta taya firaministan kasar Indiya Narendra Modi murnar samun nasara a zaben kasar, a cewar Mao Ning. Ta kara da cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasar Indiya wajen ci gaba da tabbatar da moriyar kasashen biyu da al’ummominsu, da kuma sa kaimi ga bunkasuwar huldar dake tsakanin kasashen biyu bisa turba mai inganci da kwanciyar hankali.

Kasar Sin ta kuduri aniyar wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsibirin Koriya, kuma tana adawa da duk wata magana ko aiki da ke kara ta’azzara rikici a tsibirin, a cewar Mao Ning biyo bayan shawarar da kasar Koriya ta Kudu ta yanke ta dakatar da yarjejeniyar soja da kasar Koriya ta Arewa da ita suka daddale a ranar 19 ga watan Satumban shekarar 2018. (Yahaya)

 

Labarai Masu Nasaba

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Li QiangWang yiXin hua
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Musunta Zargin Kashe Jama’a A Kudu Maso Gabas

Next Post

Zargin Da Ke Tattare Da Kalaman Da ‘Yan Siyasar Philippines Ke Yi Kan Kasar Sin

Related

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
Daga Birnin Sin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

11 hours ago
Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

13 hours ago
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

13 hours ago
Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

15 hours ago
Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

15 hours ago
An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana

17 hours ago
Next Post
Zargin Da Ke Tattare Da Kalaman Da ‘Yan Siyasar Philippines Ke Yi Kan Kasar Sin

Zargin Da Ke Tattare Da Kalaman Da ‘Yan Siyasar Philippines Ke Yi Kan Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

June 14, 2025
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

June 14, 2025
APC

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

June 14, 2025
Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

June 13, 2025
jam'iyyu

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

June 13, 2025
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

June 13, 2025
Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

June 13, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

June 13, 2025
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

June 13, 2025
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.