• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

MOFA: Batun Taiwan Ba Ya Bukatar Tsangwama Daga Waje

by CGTN Hausa
12 months ago
in Daga Birnin Sin
0
MOFA: Batun Taiwan Ba Ya Bukatar Tsangwama Daga Waje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya fada a wata hira da ya yi cewa, idan aka samu rikici na soji tsakanin bangarori biyu na mashigin tekun Taiwan, bai kawar da yiwuwar shiga tsakani na sojojin Amurka ba. Dangane da hakan, yayin da take mayar da martani, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana a gun taron manema labarai da aka saba gudanarwa a yau 5 ga wata cewa, Taiwan wani yanki ne da ba zai taba rabuwa da kasar Sin ba, kuma batun Taiwan lamari ne na cikin gida na kasar Sin wanda ba ya lamuntar tsoma baki daga waje.

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Sun Weidong zai jagoranci wata tawaga da za ta halarci taron manyan jami’an ASEAN da Sin da Japan da Koriya ta Kudu, da taron manyan jami’ai na gabashin Asiya, da taron manyan jami’ai na dandalin tattaunawar ASEAN da za a yi a Vientiane a ranar 7 zuwa 8 ga wata. Mao Ning ta kara da cewa, kasar Sin na fatan yin mu’amala mai zurfi tare da dukkan bangarorin da za su halarci tarukan, domin sa kaimi ga samun sabbin ci gaba a hadin gwiwar dake tsakanin kasashen gabashin Asiya, da ba da gudummawa sosai wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da samun ci gaba tare.

  • Sin Tana Son Yin Aiki Tare Da Hukumar IAEA Don Tabbatar Da Shawarar Ci Gaban Duniya Da Shawarar Tsaron Duniya
  • Wang Yi: Karin Kasashe Na Nuna Goyon Baya, Za A Kyautata Fatan Samun Zaman Lafiya

Ban da haka kuma, kasar Sin ta taya firaministan kasar Indiya Narendra Modi murnar samun nasara a zaben kasar, a cewar Mao Ning. Ta kara da cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasar Indiya wajen ci gaba da tabbatar da moriyar kasashen biyu da al’ummominsu, da kuma sa kaimi ga bunkasuwar huldar dake tsakanin kasashen biyu bisa turba mai inganci da kwanciyar hankali.

Kasar Sin ta kuduri aniyar wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsibirin Koriya, kuma tana adawa da duk wata magana ko aiki da ke kara ta’azzara rikici a tsibirin, a cewar Mao Ning biyo bayan shawarar da kasar Koriya ta Kudu ta yanke ta dakatar da yarjejeniyar soja da kasar Koriya ta Arewa da ita suka daddale a ranar 19 ga watan Satumban shekarar 2018. (Yahaya)

 

Labarai Masu Nasaba

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Li QiangWang yiXin hua
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Musunta Zargin Kashe Jama’a A Kudu Maso Gabas

Next Post

Zargin Da Ke Tattare Da Kalaman Da ‘Yan Siyasar Philippines Ke Yi Kan Kasar Sin

Related

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai
Daga Birnin Sin

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

20 hours ago
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

21 hours ago
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

22 hours ago
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

24 hours ago
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 
Daga Birnin Sin

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

1 day ago
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

1 day ago
Next Post
Zargin Da Ke Tattare Da Kalaman Da ‘Yan Siyasar Philippines Ke Yi Kan Kasar Sin

Zargin Da Ke Tattare Da Kalaman Da ‘Yan Siyasar Philippines Ke Yi Kan Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

June 5, 2025
Malta Guinness

Bikin Bukin Sallar Da Malta Guinness

June 5, 2025
Hukumar kashe gobara

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

June 5, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

June 5, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.