• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu Leka Shirin “Bunkasa Tagomashin Kirkirarriyar Basira Ta AI” Na Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Mu Leka Shirin “Bunkasa Tagomashin Kirkirarriyar Basira Ta AI” Na Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A duk fadin duniya a halin yanzu, kowa ya amince da cewa, fasahar kirkirarriyar basira ta AI ta taho da guguwar sauye-sauye da suka zama wajibi masu neman ci gaba ta ko wace fuska su runguma, wadanda suka tsaya sanya kuwa, za a bar su a baya suna tsintar hula.

Kasar Sin ta fahimci yadda fasahar AI ke da matukar alfanu wajen zamanantar da masana’antun da ake da su yanzu, da kuma ba da damar kafa sabbi. Rahoton ayyukan gwamnatin Sin na shekarar 2025 ya muhimmanta shirin “bunkasa tagomashin kirkirarriyar basira ta AI” bisa yadda kasar ta kudiri aniyar zage damtse wajen gwama fasahohin zamani da ayyukan masana’antu da kuma kasuwanci. Wannan ba kawai kasar Sin zai amfanar ba har da duniya, domin kasar ce ta fi ko wacce yawan masana’antu a duniya kuma babu wadda ta kamo ta a cikin shekaru 15 da suka gabata.

  • Kasar Sin Za Ta Yi Ramuwar Gayya Kan Takunkumin Biza Da Amurka Ta Kakaba Wa Jami’anta
  • Trump Na Son Yin Wa’adi Na Uku Na Shugabancin Amurka

Kasar ta kafa masana’antu na gwajin fasahar AI na kasa 421, kana da wasu masana’antu masu aiki da fasahar sadarwa ta 5G fiye da 4,000. Gwamnatin kasar ta kuma yi alkawarin tallafa wa duk wani yunkuri na amfani da fasahar AI ta gwaji a manyan masana’antu tare da kakkafa sabbin sassan cibiyoyin sarrafa kayayyakin aiki na zamani wadanda suka kunshi motocin sabbin makamashi masu aiki da fasaha, da wayoyin salula da kwamfutoci masu aiki da AI da kuma mutum-mutumi masu fasaha.

Sakamakon hobbasar da kasar ke yi a bangaren kere-kere da kirkire-kirkire tun daga kan doron kasa har zuwa sararin samaniya, ‘yan kasuwar ketare da suka halarci taron dandalin raya kasar Sin (CDF) a birnin Beijing, da taron shekara-shekara na dandalin Boao na Asiya (BFA) na 2025, dukkansu sun sha alawashin fadada zuba jarinsu ko kuma kiyaye abin da suka zuba.

Shugaban kamfanin Siemens, Roland Busch daga Jamus, da Shugaban kamfanin lantarki na Schneider Electric, Jean-Pascal Tricoire daga Faransa da kuma Shugaban Kamfanin AstraZeneca, Pascal Soriot daga Burtaniya, sun yi amannar kasar Sin tana da mafita a kan rudanin tattalin arziki na duniya bisa yadda ta zama katafariyar cibiyar manyan fasahohin zamani. Wannan ya sa ake da tabbacin, kwalliya za ta biya kudin sabulu bayan kammala aiwatar da cikakken shirin “bunkasa tagomashin kirkirarriyar basira ta AI” ba ga kasar Sin ba kawai har ma da sauran sassan duniya.

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Neman “’Yancin Kan Taiwan” Da Jam’iyyar DPP Ke Yi Zai Ci Tura

Next Post

Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Galadiman Kano, Abbas Sanusi

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

2 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

4 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

4 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

20 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

21 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

23 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Galadiman Kano, Abbas Sanusi

Tinubu Ya Yi Ta'aziyyar Rasuwar Galadiman Kano, Abbas Sanusi

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Ai

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.