• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dukafa Kawo Karshen Matsalar Wuta A Arewa Maso Gabas – Gwamna Inuwa

by Khalid Idris Doya
1 year ago
gombe

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya tabbatar da cewa, gwamnoni arewa maso gabas sun dukufa wajen ganin sun shawo kan matsalar rashin wutar lantarki da ta ki ci ta ki jinyewa a yankin, a musamman a ‘yan kwanakin nan.

Inuwa ya shaida haka ne ga manema labarai jim kadan bayan ganawarsa da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a ranar Talata a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

  • Majalisa Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Wutar Lantarki A Arewa Maso Gabas
  • Gwamnan Zamfara Ya Ƙara Mafi Ƙarancin Albashi Daga N7,000 Zuwa N30,000, Za A Fara Biya Daga Yuni

Ya ce, rarraba duk wani abu da ya shafi wutar lantarki ya kasance ne cikin jerin kebabbun hakkoki na gwamnatin tarayya, amma yanzu tun da an samar da sabuwar dokar wutar lantarki, jihohi na iya samarwa da rarrabawa.

Gwamnan ya kara da cewa, “Ko a taron Gwamnonin Arewa Maso Gabas na karshen nan da muka kammala kwanan nan, mun yanke shawarar cewa kowannenmu ya samar da Megawatts 10 na wutar lantarki daga hasken rana, kuma dukkaninmu muna da damar yin aiki da sabuwar dokar samar da wutar lantarkin, mun san cewa daga yanzu dogaro kan kaifi daya kawai ba zai kai mu ba. Duk abin da muke da shi bai iya fitar da mu daga wannan hali ba”.

Don haka ya tabbatar da cewa yanzu akwai hanya mafi inganci, kuma gwamnonin su na fatan shawo kan matsalar wacce ta dade tana ci wa jama’arsu tuwo a kwarya.

LABARAI MASU NASABA

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Gwamna Yahaya ya yi wa shugaban Nijeriyan bayanin abubuwan da ke faruwa a Jihar Gombe karkashin jagorancinsa cikin shekaru biyar da suka gabata, da irin tasirin shugabancinsa da kuma kokarin inganta harkokin mulki da ci gaba a matakin jiha.

Gwamnan ya bayyana irin shirye-shirye da tsare-tsaren da gwamnatinsa ta dauka tun bayan hawansa mulki a 2019.

Ya bayyana irin nasarorin da ya samu a bangarori daban-daban da suka hada da kiwon lafiya, da ilimi, da samar da ababen more rayuwa, da gina al’umma da kuma inganta tattalin arziki.

Ya yi kuma alkawarin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki tukuru don ganin ta cimma dukkanin shirye-shiryen da ta tsara a cikin sauran shekaru ukun da suka rage mata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Hatsarin Jiragen Ruwa
Labarai

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum
Manyan Labarai

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
Labarai

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Next Post
Gidan Gwamnatin Kano

Yanzu-Yanzu: Sarki Sunusi Ya Isa Gidan Gwamnatin Kano

LABARAI MASU NASABA

Hatsarin Jiragen Ruwa

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

October 26, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

October 26, 2025
Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.