• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Kawo Jam’iyyar AAC Ne Domin Al’ummar Adamawa – Doubli

by Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
AAC

An bayyana gabatar da jam’iyyar African Action Congress (AAC) a Jihar Adamawa domin al’umma ba za su yi nadamar zabenta a 2027 ba.

Sakataren tsare-tsaren jam’iyyar a jihar, Aliyu Umar Doubli, ya bayyana haka ga manema labarai a Yola.

  • Ziyarar Shugaba Xi A Serbia Ta Haifar Da Dimbin Nasarori
  • Sabon Harajin Tsaron Yanar Gizo Bai Shafi Hada-hadar Kudi 16 Ba – CBN

Ya ce duba da halin matsi da kalubalen da al’ummar Nijeriya ke ciki, jam’iyyar AAC ce za ta fitar da kasar daga halin kunci.

Ya ci gaba da cewa “Al’ummar Nijeriya suna bukatar jam’iyyar mutanen kwarai jam’iyya mai manufofi, manufofin da za su ceto al’ummar wannan kasa daga cikin kunci da kangin talaucin da suke ciki.

“Jam’iyyu da dama suna shirin narkewa su shigo jam’iyyar AAC, kana tsammanin jam’iyyar nan ta fito ne haka kawai? Jam’iyyar AAC ta fito ne don ta ceto ‘yan kasa ta ceto al’umma ta fitar da su daga cikin kangin da aka jefa su.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

“An kafa AAC ne domin jama’a, don haka al’umma su zo su hanzarta shigarta, domin jam’iyya ce ta jama’a kuma ana sauraron jama’a ana kuma daukar matakai da ya dace da jama’a don samun sauki da halin kokan da suke yi.

“Wannan sabuwar jam’iyya ce da za ta raba ku da halin kuncin da kuke ciki, ta zo da kyawawan manufofi a kowane fanni, tattalin arziki, kiwon lafiya, Ilimi, harkokin noma da kyautata rayuwar ‘yan kasa” in ji Doubli.

Da yake magana kan batun mafi karancin albashi, Aliyu Umar Doubli, ya ce “Ma’aikaci ya zama abin tausayi, ya zama abin wofantarwa, gwamnati ba ta dauke shi a bakin komai ba, an cire tallafi an kara kudin makaranta, ga tsadar rayuwa, ka fada min mene ne talaka yake mora daga gwamnati?

“Wannan ya sa muke kokarin nuna wa talaka, mu bi duk hanyar da ya kamata domin talaka ya samu sassauci da saukin rayuwa, wannan yanayin ya jefa kasar cikin rashin tabbas, ba a san inda Nijeriya ta dosa ba” in ji Doubli.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu
Siyasa

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Next Post
Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa

Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da 'Yarsa

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.