• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Kawo Jam’iyyar AAC Ne Domin Al’ummar Adamawa – Doubli

by Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
in Siyasa
0
Mun Kawo Jam’iyyar AAC Ne Domin Al’ummar Adamawa – Doubli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An bayyana gabatar da jam’iyyar African Action Congress (AAC) a Jihar Adamawa domin al’umma ba za su yi nadamar zabenta a 2027 ba.

Sakataren tsare-tsaren jam’iyyar a jihar, Aliyu Umar Doubli, ya bayyana haka ga manema labarai a Yola.

  • Ziyarar Shugaba Xi A Serbia Ta Haifar Da Dimbin Nasarori
  • Sabon Harajin Tsaron Yanar Gizo Bai Shafi Hada-hadar Kudi 16 Ba – CBN

Ya ce duba da halin matsi da kalubalen da al’ummar Nijeriya ke ciki, jam’iyyar AAC ce za ta fitar da kasar daga halin kunci.

Ya ci gaba da cewa “Al’ummar Nijeriya suna bukatar jam’iyyar mutanen kwarai jam’iyya mai manufofi, manufofin da za su ceto al’ummar wannan kasa daga cikin kunci da kangin talaucin da suke ciki.

“Jam’iyyu da dama suna shirin narkewa su shigo jam’iyyar AAC, kana tsammanin jam’iyyar nan ta fito ne haka kawai? Jam’iyyar AAC ta fito ne don ta ceto ‘yan kasa ta ceto al’umma ta fitar da su daga cikin kangin da aka jefa su.

Labarai Masu Nasaba

ÆŠaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

“An kafa AAC ne domin jama’a, don haka al’umma su zo su hanzarta shigarta, domin jam’iyya ce ta jama’a kuma ana sauraron jama’a ana kuma daukar matakai da ya dace da jama’a don samun sauki da halin kokan da suke yi.

“Wannan sabuwar jam’iyya ce da za ta raba ku da halin kuncin da kuke ciki, ta zo da kyawawan manufofi a kowane fanni, tattalin arziki, kiwon lafiya, Ilimi, harkokin noma da kyautata rayuwar ‘yan kasa” in ji Doubli.

Da yake magana kan batun mafi karancin albashi, Aliyu Umar Doubli, ya ce “Ma’aikaci ya zama abin tausayi, ya zama abin wofantarwa, gwamnati ba ta dauke shi a bakin komai ba, an cire tallafi an kara kudin makaranta, ga tsadar rayuwa, ka fada min mene ne talaka yake mora daga gwamnati?

“Wannan ya sa muke kokarin nuna wa talaka, mu bi duk hanyar da ya kamata domin talaka ya samu sassauci da saukin rayuwa, wannan yanayin ya jefa kasar cikin rashin tabbas, ba a san inda Nijeriya ta dosa ba” in ji Doubli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AACAdamawaJam'iyyaSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gabatar Da Shirin Talabijin Mai Suna Labarun Da Xi Jinping Ya Fi So A Hungary

Next Post

Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa

Related

Labarai

ÆŠaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

14 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

18 hours ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

3 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

4 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

5 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

6 days ago
Next Post
Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa

Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da 'Yarsa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

ÆŠaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.