• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Kawo Jam’iyyar AAC Ne Domin Al’ummar Adamawa – Doubli

byMuh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
AAC

An bayyana gabatar da jam’iyyar African Action Congress (AAC) a Jihar Adamawa domin al’umma ba za su yi nadamar zabenta a 2027 ba.

Sakataren tsare-tsaren jam’iyyar a jihar, Aliyu Umar Doubli, ya bayyana haka ga manema labarai a Yola.

  • Ziyarar Shugaba Xi A Serbia Ta Haifar Da Dimbin Nasarori
  • Sabon Harajin Tsaron Yanar Gizo Bai Shafi Hada-hadar Kudi 16 Ba – CBN

Ya ce duba da halin matsi da kalubalen da al’ummar Nijeriya ke ciki, jam’iyyar AAC ce za ta fitar da kasar daga halin kunci.

Ya ci gaba da cewa “Al’ummar Nijeriya suna bukatar jam’iyyar mutanen kwarai jam’iyya mai manufofi, manufofin da za su ceto al’ummar wannan kasa daga cikin kunci da kangin talaucin da suke ciki.

“Jam’iyyu da dama suna shirin narkewa su shigo jam’iyyar AAC, kana tsammanin jam’iyyar nan ta fito ne haka kawai? Jam’iyyar AAC ta fito ne don ta ceto ‘yan kasa ta ceto al’umma ta fitar da su daga cikin kangin da aka jefa su.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

“An kafa AAC ne domin jama’a, don haka al’umma su zo su hanzarta shigarta, domin jam’iyya ce ta jama’a kuma ana sauraron jama’a ana kuma daukar matakai da ya dace da jama’a don samun sauki da halin kokan da suke yi.

“Wannan sabuwar jam’iyya ce da za ta raba ku da halin kuncin da kuke ciki, ta zo da kyawawan manufofi a kowane fanni, tattalin arziki, kiwon lafiya, Ilimi, harkokin noma da kyautata rayuwar ‘yan kasa” in ji Doubli.

Da yake magana kan batun mafi karancin albashi, Aliyu Umar Doubli, ya ce “Ma’aikaci ya zama abin tausayi, ya zama abin wofantarwa, gwamnati ba ta dauke shi a bakin komai ba, an cire tallafi an kara kudin makaranta, ga tsadar rayuwa, ka fada min mene ne talaka yake mora daga gwamnati?

“Wannan ya sa muke kokarin nuna wa talaka, mu bi duk hanyar da ya kamata domin talaka ya samu sassauci da saukin rayuwa, wannan yanayin ya jefa kasar cikin rashin tabbas, ba a san inda Nijeriya ta dosa ba” in ji Doubli.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa

Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da 'Yarsa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version