• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Bukatar Matakin Gaggawa Kan Yaki Da Ta’addanci A Yammacin Afirka –Buhari

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci a gaggauta kaddamar da mataki kan yaki da ta’addanci a yankin yammacin Afirka.

Shugaban kasan ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi a wurin taron shugabannin ECOWAS karo na 62 wanda ya gudana a Abuja. Ya kara da cewa akwai bukatar sauya salon yaki da ‘yan ta’adda a yankin yammacin Afirka.

  • Allah Ya Yi Wa ‘Yar Uwar Shugaba Buhari, Hajiya Laraba Rasuwa

A cewarsa, wannan yunkuri zai karfafa kokarin gwamnatocin yanki wajen tabbatar da ci gaba mai dorewa a yammacin Afirka. Ya yi kira ga sabon tawagar ECOWAS wanda Dakta Omar Alieu Toure yake jagoranta kan gaggauta kammala nazari na sake fasalin kungiyar domin samun inganta yankin yammacin Afirka.

“Dole ne kungiyar ECOWAS ta gudanar da aiki ba dare ba rana wajen ganin an kammala yin nazari kan sauya fasalin ka’idojin shugabanci da na dimokuradiyya a yankin yammacin Afirka, domin karfafa kokarinmu wajen gudanar da shugabanci mai inganci ga kasashenmu.”

Da yake yi wa shugabannin yankin maraba, Buhari ya ce taron wannan shekarar shi ne na 8 da Nijeriya ke shiryawa.
“Dukkan wadannan taruka ciki har da na wannan shekara Nijeriya ce ke shiryawa wanda hakan ke kara karfafa dangantakarmu domin bullo da hanyoyin magance matsalolin kasashenmu da kuma al’ummominmu,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Shugaban Buhari ya jinjina wa takwaransa na kasar Ghana, Kuffour Addo-Nana wanda ya kasance tsohon shugaban kungiyar bisa shugabancinsa da taya murna ga Shugaban Guinea Bissau, Umaro Embalo kan tabbatar da daukar ragamar shugabancin kungiyar.”

Buhari ya gode wa shugabannin bisa goyon bayansu wajen rawar da suka taka lokacin cutar Korona kan hadin kai yankunan yammacin Afirka.

Tun da farko dai a harabar sabon shalkwatan ECOWAS, Buhari ya nuna godiyarsa ga gwamnatin China bisa tallafin kudade da kayan aiki wajen gina shalkwatan kungiyar.

Gini da aka sanya wa suna idon yammacin Afirka ana tsammanin za a kammala shi ne nan da watanni 26, yana da manyan cibiyoyi guda uku wadanda suka hada da na shalkwatan kungiyar ECOWAS da kotun gungiyar da majalisarta.

A cewar shugaban kasan, “Da ma muna jiran wannan rana tun 10 ga watan Yulin 2019 lokacin da ECOWAS da mutanen China suka rattaba hannu kan kaddamar da kyautar difolomasiyya ga kasashen yammacin Afirka.
A nasa jawabin, Jakadar kasar China a Nijeriya, Cui Jianchun ya ce, “Tallafin gina sabon shalkwantan ECOWAS yana zuwa ne sakamakon kawance da kasar China take da shi da kasashen yammacin Afirka.

“Za mu ci gaba da bunkasa kawance tsakanin China da Afirka, sannan a shirye muke mu bayar da tallafi wajen ci gaban Afirka zuwa mataki na gaba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Barazanar Kone-konen Ofisoshin INEC Ga Zaben 2023

Next Post

Batun Yara Miliyan 20 Da Ke Gararamba A Titunan Nijeriya Ba Su Zuwa Makaranta Ba

Related

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

2 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

5 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

7 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

9 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

12 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

23 hours ago
Next Post
NIjeriya

Batun Yara Miliyan 20 Da Ke Gararamba A Titunan Nijeriya Ba Su Zuwa Makaranta Ba

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.