• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Bukatar Matakin Gaggawa Kan Yaki Da Ta’addanci A Yammacin Afirka –Buhari

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci a gaggauta kaddamar da mataki kan yaki da ta’addanci a yankin yammacin Afirka.

Shugaban kasan ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi a wurin taron shugabannin ECOWAS karo na 62 wanda ya gudana a Abuja. Ya kara da cewa akwai bukatar sauya salon yaki da ‘yan ta’adda a yankin yammacin Afirka.

  • Allah Ya Yi Wa ‘Yar Uwar Shugaba Buhari, Hajiya Laraba Rasuwa

A cewarsa, wannan yunkuri zai karfafa kokarin gwamnatocin yanki wajen tabbatar da ci gaba mai dorewa a yammacin Afirka. Ya yi kira ga sabon tawagar ECOWAS wanda Dakta Omar Alieu Toure yake jagoranta kan gaggauta kammala nazari na sake fasalin kungiyar domin samun inganta yankin yammacin Afirka.

“Dole ne kungiyar ECOWAS ta gudanar da aiki ba dare ba rana wajen ganin an kammala yin nazari kan sauya fasalin ka’idojin shugabanci da na dimokuradiyya a yankin yammacin Afirka, domin karfafa kokarinmu wajen gudanar da shugabanci mai inganci ga kasashenmu.”

Da yake yi wa shugabannin yankin maraba, Buhari ya ce taron wannan shekarar shi ne na 8 da Nijeriya ke shiryawa.
“Dukkan wadannan taruka ciki har da na wannan shekara Nijeriya ce ke shiryawa wanda hakan ke kara karfafa dangantakarmu domin bullo da hanyoyin magance matsalolin kasashenmu da kuma al’ummominmu,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

Shugaban Buhari ya jinjina wa takwaransa na kasar Ghana, Kuffour Addo-Nana wanda ya kasance tsohon shugaban kungiyar bisa shugabancinsa da taya murna ga Shugaban Guinea Bissau, Umaro Embalo kan tabbatar da daukar ragamar shugabancin kungiyar.”

Buhari ya gode wa shugabannin bisa goyon bayansu wajen rawar da suka taka lokacin cutar Korona kan hadin kai yankunan yammacin Afirka.

Tun da farko dai a harabar sabon shalkwatan ECOWAS, Buhari ya nuna godiyarsa ga gwamnatin China bisa tallafin kudade da kayan aiki wajen gina shalkwatan kungiyar.

Gini da aka sanya wa suna idon yammacin Afirka ana tsammanin za a kammala shi ne nan da watanni 26, yana da manyan cibiyoyi guda uku wadanda suka hada da na shalkwatan kungiyar ECOWAS da kotun gungiyar da majalisarta.

A cewar shugaban kasan, “Da ma muna jiran wannan rana tun 10 ga watan Yulin 2019 lokacin da ECOWAS da mutanen China suka rattaba hannu kan kaddamar da kyautar difolomasiyya ga kasashen yammacin Afirka.
A nasa jawabin, Jakadar kasar China a Nijeriya, Cui Jianchun ya ce, “Tallafin gina sabon shalkwantan ECOWAS yana zuwa ne sakamakon kawance da kasar China take da shi da kasashen yammacin Afirka.

“Za mu ci gaba da bunkasa kawance tsakanin China da Afirka, sannan a shirye muke mu bayar da tallafi wajen ci gaban Afirka zuwa mataki na gaba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Barazanar Kone-konen Ofisoshin INEC Ga Zaben 2023

Next Post

Batun Yara Miliyan 20 Da Ke Gararamba A Titunan Nijeriya Ba Su Zuwa Makaranta Ba

Related

buhari
Labarai

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

52 minutes ago
Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu
Labarai

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

57 minutes ago
Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle
Labarai

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

4 hours ago
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya
Manyan Labarai

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

5 hours ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

19 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

21 hours ago
Next Post
NIjeriya

Batun Yara Miliyan 20 Da Ke Gararamba A Titunan Nijeriya Ba Su Zuwa Makaranta Ba

LABARAI MASU NASABA

buhari

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

May 10, 2025
Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

May 10, 2025
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

May 10, 2025
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

May 10, 2025
Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

May 10, 2025
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

May 10, 2025
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.