• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Fara Shirye-Shiryen Hada Kayana Don Komawa Daura Nan Da Watanni Biyar 5 —Buhari

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana cewar a yanzu haka har ya fara shirye-shiryen hada kayansa domin komawa garinsa ta asali wato Daura da ke jihar Katsina nan da watanni biyar bayan karewar wa’adin mulkinsa. 

 

Buhari ya shaida hakan ne a ranar Talata a birnin tarayya Abuja sa’ilin da ya amshi bakwancin mambobin Jam’iyyatu Ansaridden (Attijaniyya), inda ya jinjina wa kungiyar a bisa kokarin da suke yi waje bunkasa hadin kan addinai a fadin kasar nan.

  • Buhari Ya Ba Ni Tabbacin Za A Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Atiku

Tawagar kungiyar ‘yan darikar wadanda suka ziyararci shugaba Buhari a karkashin jagorancin Sheikh Muhammad Khalifa Niass, Khalifan Jam’iyyatu Ansaridden (Attijaniyya), Buharin ya shaida musu cewa, yana matukar ganin muhimmancin rawar da suke takawa wajen inganta zaman lafiya a kasashen Afrika.

 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Shugaba Buhari wanda ya gode wa mambobin kungiyar a bisa addu’o’in da suka yi ta yi wa gwamnatinsa da kasa baki daya, kamar yadda hadimin shugaban kansan a bangaren yada labarai Malam Garba Shehu ya nakalto ta cikin wata sanarwar da ya raba wa ‘yan jarida.

 

Shugaban ya shaida wa bakin nasa cewa yana ta kan kimtsa kayansa da shirin komawa Daura da zarar wa’adinsa ya kare.

 

A yayin ziyarar, malamin addinin musulunci, Sheikh Tijjani Shehul Hadi Almauritany ya yi wa shugaban kasa da Nijeriya addu’a ta musamman, yayin da kuma Sheikh Abdullahi Lamine ya rero ayoyi daga cikin Alkur’ani Mai girma.

 

A jawabinsa Khalifan kungiyar, Sheikh Niass, ya yi tilawar tarihin Annabi Muhammad (SAW) da irin darrrusan da ya dace al’ummar musulmai su koya daga rayuwarsa.

 

Ya nanata muhimmancin tuna ta hakika ga masu aikata laifukan da suka saba wa Ubangiji.

 

Ya kuma sha alwashin cewa kungiyar za ta cigaba da kokarin hada kan al’umma da bunkasa zaman lafiya kamar yadda addinin musulunci da Annabi Muhammad suka koyar.

 

Khalifah Niass ya kuma ba da labarin irin kusancin da mahaifinsa, Sheikh Ibrahim Niass ya yi da Nijeriya da al’ummarta, wanda ya kai shekaru saba’in, inda ya ce iyalin sun kuduri aniyar ci gaba da kulla alaka domin kyautata zamantakewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?
Ra'ayi Riga

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Labarai

Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 

October 23, 2025
Next Post
Jimillar Jarin Da Asusun Raya Kasashen Sin Da Afirka Ya Zuba Ta Zarce Dalar Amurka Biliyan 5 

Jimillar Jarin Da Asusun Raya Kasashen Sin Da Afirka Ya Zuba Ta Zarce Dalar Amurka Biliyan 5 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 

October 23, 2025
Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

October 23, 2025
Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

October 23, 2025
Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

October 23, 2025
Yajin aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja 

October 23, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.