• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Fara Shirye-Shiryen Hada Kayana Don Komawa Daura Nan Da Watanni Biyar 5 —Buhari

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Na Fara Shirye-Shiryen Hada Kayana Don Komawa Daura Nan Da Watanni Biyar 5 —Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana cewar a yanzu haka har ya fara shirye-shiryen hada kayansa domin komawa garinsa ta asali wato Daura da ke jihar Katsina nan da watanni biyar bayan karewar wa’adin mulkinsa. 

 

Buhari ya shaida hakan ne a ranar Talata a birnin tarayya Abuja sa’ilin da ya amshi bakwancin mambobin Jam’iyyatu Ansaridden (Attijaniyya), inda ya jinjina wa kungiyar a bisa kokarin da suke yi waje bunkasa hadin kan addinai a fadin kasar nan.

  • Buhari Ya Ba Ni Tabbacin Za A Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Atiku

Tawagar kungiyar ‘yan darikar wadanda suka ziyararci shugaba Buhari a karkashin jagorancin Sheikh Muhammad Khalifa Niass, Khalifan Jam’iyyatu Ansaridden (Attijaniyya), Buharin ya shaida musu cewa, yana matukar ganin muhimmancin rawar da suke takawa wajen inganta zaman lafiya a kasashen Afrika.

 

Labarai Masu Nasaba

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

Shugaba Buhari wanda ya gode wa mambobin kungiyar a bisa addu’o’in da suka yi ta yi wa gwamnatinsa da kasa baki daya, kamar yadda hadimin shugaban kansan a bangaren yada labarai Malam Garba Shehu ya nakalto ta cikin wata sanarwar da ya raba wa ‘yan jarida.

 

Shugaban ya shaida wa bakin nasa cewa yana ta kan kimtsa kayansa da shirin komawa Daura da zarar wa’adinsa ya kare.

 

A yayin ziyarar, malamin addinin musulunci, Sheikh Tijjani Shehul Hadi Almauritany ya yi wa shugaban kasa da Nijeriya addu’a ta musamman, yayin da kuma Sheikh Abdullahi Lamine ya rero ayoyi daga cikin Alkur’ani Mai girma.

 

A jawabinsa Khalifan kungiyar, Sheikh Niass, ya yi tilawar tarihin Annabi Muhammad (SAW) da irin darrrusan da ya dace al’ummar musulmai su koya daga rayuwarsa.

 

Ya nanata muhimmancin tuna ta hakika ga masu aikata laifukan da suka saba wa Ubangiji.

 

Ya kuma sha alwashin cewa kungiyar za ta cigaba da kokarin hada kan al’umma da bunkasa zaman lafiya kamar yadda addinin musulunci da Annabi Muhammad suka koyar.

 

Khalifah Niass ya kuma ba da labarin irin kusancin da mahaifinsa, Sheikh Ibrahim Niass ya yi da Nijeriya da al’ummarta, wanda ya kai shekaru saba’in, inda ya ce iyalin sun kuduri aniyar ci gaba da kulla alaka domin kyautata zamantakewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin Kasar Amurka Za Ta Iya Cika Alkawarinta?

Next Post

Jimillar Jarin Da Asusun Raya Kasashen Sin Da Afirka Ya Zuba Ta Zarce Dalar Amurka Biliyan 5 

Related

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

1 hour ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

2 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

3 hours ago
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

5 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

7 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

8 hours ago
Next Post
Jimillar Jarin Da Asusun Raya Kasashen Sin Da Afirka Ya Zuba Ta Zarce Dalar Amurka Biliyan 5 

Jimillar Jarin Da Asusun Raya Kasashen Sin Da Afirka Ya Zuba Ta Zarce Dalar Amurka Biliyan 5 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

September 14, 2025
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

September 14, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

September 14, 2025
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

September 14, 2025
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.