ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Taba Zuwa Gidan Yari A Kan Fim Din Da Na Shirya – Ali Ibrahim

by Rabi'at Sidi Bala
3 years ago
Fim

LABARAI MASU NASABA

Jarumin Nollywood Olu Jacobs Ya Rasu Yana Da Shekaru 84

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Daya daga cikin fitattun Jaruman, wanda ya shafe shekaru ashirin da biyar a cikin masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, ALI IBRAHIM wanda aka fi sani da ALI DAWAYYA. Ya bayyana wa masu karatu irin kalubalen da ya fuskanta cikin masana’antar, tare da irin rawar da ya ke takawa a cikin masana’antar ta Kannywood, har ma da wasu batutuwan masu yawa wadanda suka shafi sana’arsa ta fim. Ga dai tattaunawar tare da RABI’AT SIDI BALA kamar haka:

Da farko za ka fara fadawa masu karatu cikakken sunanka tare da sunan da aka fi saninka da shi.

Sunana Ali Ibrahim wanda aka fi sani da Ali Dawayya.

Me ya sa ake kiranka da Ali Dawayya, shin kana da alaka ko dangantaka da Rukayya Dawayya ne?

Abun da ya sa ake ce mun Ali Dawayya shi ne; Akwai wani fim mai suna ‘Miras A Jo’s’ fim din kamfanin ‘Almah Production’ ni ne ‘light Man’ na fim din, sai janareto din da muke aiki da shi ya lalace na kasa gyarawa, ina ta zurga-zurga duk nayi gumi, sai Ali Nuhu ya ce; “Kanata kaiwa da dawowa ka ki zama, wannan ai kai ne Dawayya, sunan wani fim din Iyan Tama da zai fara”. Shi ne kowa ya fashe da dariya daga nan idan na zo wucewa a lokeshan din sai a yi ta yi mun dan kira ana cewa; “Dawayya”, idan na juyo sai a yi shiru, da’ na fara cewa bana son sunan sai ya zamar mun abun zolaya, amma ba ni da alaka da Rukayya Dawayya sai dai ta sama, da kuma addini daya.

Ko za ka fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinka?

Ni haifaffen garin Jo’s ne a can aka haife ni, a can nayi karatu daga nan sai ogana dan uwana Ahmad S. Nuhu na zauna a gidan yallabai Ali Nuhu ya taho da ni Kano na fara zama, amma Kano garinmu ne anan aka haifi babana a Dawakin Kudu LGA, cikin Tsakuwa. Bayan na zama dan Kano na fara koyar ‘light’ a wajen Malam Yakubu daga nan na dawo wajan Umar Gotip marigayi, daga nan sai na zama ogan kaina, ina ci gaba da rayuwata. Sai na fara sha’awar Aktin daga nan na zama furodusa na fara fim nawa na kaina mai suna ‘Akhee’, Ajo, Faraga, Sai Na Ga Ali, Kwamachala, Zafin Nema, Kifil Kwallin Mata, Bakauye, akwai uku da na manta.

Idan na fahimce ka kana so ka ce kana da alaka da Ali Nuhu da kuma Ahmad S. Nuhu ta bangaren famili kenan, ko ya batun ya ke?

Eh! ina da shi, Ahmad S. Nuhu unguwar mu daya, kuma akwai auratayya a tsakaninmu da su, shi ne ya kawo ni, Ali Nuhu a gidanshi na zauna har sanda na yi aure kuma Ali Nuhu ya dauke ni kamar shi ya haife ni, ina ci a gidan shi ina sha, sannan kuma ya mun sutura.

Wanne irin rawa ka ke takawa a cikin masana’antar Kannywood, bayan fitowa matsayin jarumi da kuma shirya fim da ka ke yi a yanzu?

Babu irin rawar da bana takawa ni ‘Light Man’ ne kuma Akto.

Za ka yi kamar shekara nawa a cikin masana’antar?

Zan kai kamar shekara 25 tun wajen 1998 na fara.

Ya batun iyaye lokacin da ka fara sanar musu kana sha’awar fara harkar fim, shin ka samu wani kalubale daga gare su ko kuwa?

A’a ban samu matsala ba fatan alkairi suka yi min, amma abokanai na ne kawai idan suka ganni sai ki ji suna mun dan kira wai Akto, haka tun raina yana baci har ya daina.

Bayan fina-finan da ka shirya naka na kanka, ko za ka iya tuna adadin fina-finan da ka fito ciki?

Gaskiya nayi fim zai kai 200.

A wanne fim ka fara fitowa?

Zubaida na kamfanin ‘FKD PRODUCTION’, shi na fara sai kuma wanda suka fito da ni duniya ta sanni.

Wanne rawa ka taka a cikin fim din, kuma ya ka ji a lokacin, musamman yadda ka ke farkon farawa a lokacin?

Sin daya na yi Ahmad S. Nuhu ya zo siyawa Abida Mohammed ‘Prem’ na ‘girft’, gaskiya lokacin da za a sa mun ‘camera’ na ji gabana ya fadi sosai tun da ban saba ba.

Ko akwai wani kalubale da ka taba fuskanta cikin masana’antar?

Gaskiya na samu kam, tun da har gidan yari na je a kan fim dina da na yi furodusin mai suna FARAGA ta dadilin fim din Jarumai 5 ne suka je gidan yari, akwai Mansoor Saddik, Falalu Dorayi, Jibrin S. Fagge, sai ni, sai Tijjani Asase.

Me ya janyo afkuwar hakan?

Na je ‘shooting’ ne wani abokina na ce ya samo min gidan da zan yi aiki, sai ya ce “to”, ashe inda zai samo min ba sa nan sun je kauye, sai ya yi wa abokinshi magana ashe abokin nashi ba shi da inda za a yi aikin sai ya yi wa wani mai gadi magana a kan ya ba mu ‘Guess Hause’ za mu yi aiki, sai mai gidan ya ce an sace masa Pijo da miliyan 10, ya yi mana sharri saboda ya taba neman wata ‘yar fim ta ki yarda da shi shi ne ya huce a kanmu.

Za mu ci gaba a mako mai zuwa

Fim
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Alaƙata Da Adamu Zango Ta Bunƙasa A Kannywood —Jarumi Ibrahim Sodangi 
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Jarumin Nollywood Olu Jacobs Ya Rasu Yana Da Shekaru 84
Nishadi

Jarumin Nollywood Olu Jacobs Ya Rasu Yana Da Shekaru 84

September 16, 2026
Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
Next Post
Duniyar wata

Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Binciken Duniyar Wata Mai Zuwa A Tsakanin Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatinmu Za Ta Kawar Da Talauci Da Zarar An Zabe Mu – Shettima

Gwamnonin Arewa 6 Kacal Ne Suka Goyi Bayan Tinubu A 2023 – Shettima

September 16, 2026
Hanyar Ruwa Ta pinglu Ta Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN

Hanyar Ruwa Ta pinglu Ta Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN

September 16, 2026
peter

Peter Obi Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Sayi Hannun Jarin Matatar Mai Ta Dangote

September 16, 2026
Manufar Sin Kan Raba Fasahar AI Ga Saura: Hakika Mai Bayarwa Ba Ya Rasawa

Manufar Sin Kan Raba Fasahar AI Ga Saura: Hakika Mai Bayarwa Ba Ya Rasawa

September 16, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 240 Bisa Zargin Laifuka Daban-Daban A Yobe

September 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Na’urar Kiwon Lafiya Ta Sadarwa Tsakanin Kwakwalwa Da Na’ura Mai Amfani Da AI

Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Na’urar Kiwon Lafiya Ta Sadarwa Tsakanin Kwakwalwa Da Na’ura Mai Amfani Da AI

September 16, 2026
Gwamnan Kano Ya Naɗa Hafsat Kutama Mukaddashiyar Shugabar Hukumar PCACC 

Gwamnan Kano Ya Naɗa Hafsat Kutama Mukaddashiyar Shugabar Hukumar PCACC 

September 16, 2026
Rokar Gravity-1 Na Kasar Sin Ya Harba Sabbin Taurarin Dan’adam Daga Teku

Rokar Gravity-1 Na Kasar Sin Ya Harba Sabbin Taurarin Dan’adam Daga Teku

September 16, 2026
TCN Ta Samar Da Hanyar Samun Wutar Lantarki A Kebbi Ta Wucin Gadi

TCN Ta Samar Da Hanyar Samun Wutar Lantarki A Kebbi Ta Wucin Gadi

September 16, 2026
APC Ta Tsawaita Rijistar Mambobinta, Ta Ɗage Ranar Babban Taronta Na Ƙasa

APC Ta Nemi A Gudanar Da Bincike Kan Farmakin Da A Kai Ofisoshinta A Kaduna

September 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.