• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

by Shehu Yahaya
4 months ago
NAFDAC

Shugaban Kungiyar Masu Maganin Gargajiya ta Kasa (NUMHP), Dakta Kabiru Mohammad Nabargu ya bayar da tabbacin cewa Hukumar Kulla da Inganci Abinci ta Kasa ( NAFDAC) tare da kungiyarsu sun kudiri aniyar tsabtace sana’ar bayar da magungunan gargajiya a fadin kasar nan baki daya.

Dakta Kabiru ya bayyana haka ne lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a Kaduna jim kadan bayan kammala wani taron da kungiyar ta shirya tare da hadin gwiwar hukumar NAFDAC, wanda aka gudanar da shi a dakin taro na gidan Sardauna da ke Jihar Kaduna.

Ya ce ganin yadda mutane da dama da ba su san harkar maganin gargajiya ba suke shiga sana’ar wanda ke kawo cikas, inda ya ce ya zama wajibi su dauki matakin tsabtace sana’ar don kare mutuncin sana’ar tare da nuna musu muhimmacin yin rajista da hukumar NAFDAC domin tabbatar da ingancin maganin da suke sayarwa.

“Yanzu lamarin ya kai matakin da mutum zai debo itatuwa a daji ya shiga daki ya yi maganin da ba shi da rajista kuma yana sayar wa al’umma, wanda hakan ya saba wa dokar sayar da magani, saboda haka ya sa muka gayyato shugaban hukumar NAFDAC na shiyyar Arewa maso yamma da ya zo ya yi mana bayani irin tanadin da suka yi da kuma wayar da kan masu maganain gargajiya kan muhimmacin yin rajista kamin su fitar da shi kasuwa,” in ji shi.

Shugaban ya ce galibin masu fakewa da sana’ar magungunan gargajiya suna cutar mutane ba su da rajista da kungiyarsu da hukumar lafiya ko NAFDAC. Ya ce a kokarinsu na tsabtace harkar magungunan gargajiya da kare martabar sana’ar ya sanya suka hada hannu da hukumar NAFDAC domin taimaka wa duk wani mai sana’ar maganin gargajiya yin rajista domin samun natsuwa wajen gudanar da sana’arsu a fadin kasar nan baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

A nasa jawabin, shugaban hukumar NAFDAC na shiyyar Arewa maso yamma, Nantim Dadi Mullah, ya bayyana gamsuwarsa dagane da matakin da kungiyar masu maganain gargajiya ta kasa ta dauka na kawo tsabta a sana’arsu.

Ya tabbatar da cewa NAFDAC ta amince za ta yi aiki kafada da kafada da kungiyar domin ganin duk wani mai sana’ar maganin gargajiya ya yi rajista da hukumarsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gaza
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100
Labarai

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
Next Post
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

LABARAI MASU NASABA

gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
NAFDAC

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.