• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

by Shehu Yahaya
4 hours ago
in Labarai
0
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kungiyar Masu Maganin Gargajiya ta Kasa (NUMHP), Dakta Kabiru Mohammad Nabargu ya bayar da tabbacin cewa Hukumar Kulla da Inganci Abinci ta Kasa ( NAFDAC) tare da kungiyarsu sun kudiri aniyar tsabtace sana’ar bayar da magungunan gargajiya a fadin kasar nan baki daya.

Dakta Kabiru ya bayyana haka ne lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a Kaduna jim kadan bayan kammala wani taron da kungiyar ta shirya tare da hadin gwiwar hukumar NAFDAC, wanda aka gudanar da shi a dakin taro na gidan Sardauna da ke Jihar Kaduna.

Ya ce ganin yadda mutane da dama da ba su san harkar maganin gargajiya ba suke shiga sana’ar wanda ke kawo cikas, inda ya ce ya zama wajibi su dauki matakin tsabtace sana’ar don kare mutuncin sana’ar tare da nuna musu muhimmacin yin rajista da hukumar NAFDAC domin tabbatar da ingancin maganin da suke sayarwa.

“Yanzu lamarin ya kai matakin da mutum zai debo itatuwa a daji ya shiga daki ya yi maganin da ba shi da rajista kuma yana sayar wa al’umma, wanda hakan ya saba wa dokar sayar da magani, saboda haka ya sa muka gayyato shugaban hukumar NAFDAC na shiyyar Arewa maso yamma da ya zo ya yi mana bayani irin tanadin da suka yi da kuma wayar da kan masu maganain gargajiya kan muhimmacin yin rajista kamin su fitar da shi kasuwa,” in ji shi.

Shugaban ya ce galibin masu fakewa da sana’ar magungunan gargajiya suna cutar mutane ba su da rajista da kungiyarsu da hukumar lafiya ko NAFDAC. Ya ce a kokarinsu na tsabtace harkar magungunan gargajiya da kare martabar sana’ar ya sanya suka hada hannu da hukumar NAFDAC domin taimaka wa duk wani mai sana’ar maganin gargajiya yin rajista domin samun natsuwa wajen gudanar da sana’arsu a fadin kasar nan baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

A nasa jawabin, shugaban hukumar NAFDAC na shiyyar Arewa maso yamma, Nantim Dadi Mullah, ya bayyana gamsuwarsa dagane da matakin da kungiyar masu maganain gargajiya ta kasa ta dauka na kawo tsabta a sana’arsu.

Ya tabbatar da cewa NAFDAC ta amince za ta yi aiki kafada da kafada da kungiyar domin ganin duk wani mai sana’ar maganin gargajiya ya yi rajista da hukumarsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NAFDAC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Related

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

6 hours ago
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Labarai

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

8 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi

10 hours ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

12 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

12 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

14 hours ago

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.