• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NASENI Ta Dukufa Kere-kere Domin Kawo Saukin Rayuwa A Nijeriya –Khalil

by Khalid Idris Doya
2 years ago
NASENI

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Shugaban hukumar da ke gudanar da bincike kan ci gaban kimiyya da fasaha a sha’anin noma da masana’anu a Nijeriya, (NASENI), a takaice, Khalil Sulaiman Halilu, ya yi albishir wa al’ummar Nijeriya da cewa, nan da farkon shekara mai zuwa, hukumar za ta bijiro da wasu muhimman ayyukan da ta gudanar na bincike da kirkira da za su kawo saukin rayuwa ga al’umman kasar nan.

A cewarsa, hukumar ta dukufa wajen gudanar da muhimman binciken da za su kawo gagarumin sauyi da sauki wajen gudanar da harkokin rayuwa ta hanyar rungumar kimiyya da fasaha hadi da kire-kire na zamani.

  • Sama Da Kamfanoni 5,600 Ne Suka Shiga Baje Kolin Sassan Motoci Na Shanghai
  • Basirar Henry Kissinger Abu Mai Daraja Ne Ga Amurka

Halilu ya ce, hukumar ta jima tana gudanar da bincike kan kimiyya da fasaha a bangarori daban-daban kuma kwalliya tana biyan kudin sabulu domin suna fitar da abubuwa da dama da suka kera domin kyautata rayuwa.

Ya yi karin haske kan hukumar NASENI da cewa, hukuma ce da take gudanar da bincike da kirkirar abubuwan da za su kawo wa jama’a saukin rayuwa musamman na zamani kamar su harkokin kwamfuta (na’ura mai kwakwalwa), harkokin da suka shafi masana’antu da kuma harkokin da suka shafi ci gaba na kiwon lafiya da sauran bangarori.

Inda ya ce, suna gudanar da bincike domin su gano matsalolin da ake tattare da su a cikin al’umma tare da kirkiro abubuwan da za su kawo sauki, bugu da kari su kuma koyar da sauran masana’antu yadda za a yi amfani da sabbin abubuwan da aka gano domin samar da rayuwa mai sauki a cikin al’umma.

A cewarsa, a baya-bayan nan hukumar tana kera farantan wuta da ke amfani da hasken wutar rana a jihar Nasarawa kuma jama’an kasa daga sassa daban-daban na saya domin amfani da shi.

“Kuma akwai solar home system na’ura ce da ta ke bayar da hasken wuta a gida ta hanyar farantan wuta mai amfani da hasken rana da jama’a musamman a yankunan karkara ke saya domin amfanuwa.”

“A bangaren noma akwai taki na musamman da muka kirkira shi ma muna kan ganin yadda za mu samar wa manoma. Idan ka duba harkar kwamfuta akwai irin su manhajoji (softwares) kala-kala da muka yi suna ma na kawo sauki wajen gudanar da harkokin kasuwanci.”

Shugaban ya kara da cewa, a bangaren kiwon lafiya kuwa, sun kirkiro abubuwa da dama kamar su rigakafi nau’ika daban-daban dukka domin kawo wa jama’an Nijeriya saukin rayuwa.

“Muna son kafin karshen wata hudu na shekarar 2024 mutanen Nijeriya za su fara ganin irin ayyukanmu daban-daban.

“Akwai abun da ake kira technology transfer, ka ga wani kirkira a wata kasa ya maka kuma kana son ka kawo kasar ka. A Nijeriya hukumarmu ce take karban irin wannan kirkire-kirkiren da aka yi a wasu kasashe domin mu kawo su cikin gida Nijeriya tare da gyarashi zuwa irin yanayinmu da al’adunmu.

“Saboda haka mun kulla yarjejeniya da China wanda za su kawo kudi kimanin dala biliyan shida wanda za a yi amfani da shi wurin debo irin abubuwan da suka yi wanda muke da sha’awarsu a kai domin mu kawo cikin kasarmu domin taimaka wa al’umman Nijeriya,” a cewar Khalil Sulaiman.

Daga bisani ya yi kira ga matasa masu kaifin basira da suke kirkire-kirkiren abubuwa musamman a bangaren kimiyya da fasaha da zo domin hada kai da hukumar NASENI domin yin aiki mai nagarta wajen samar da saukin rayuwa musamman a bangaren bunkasa tattalin arziki da taimakon juna.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

March 8, 2025
Next Post
Shirin NPA Na Kula Da Tashoshin Jiragen Ruwa A Dunkule Zai Bunkasa Tattalin Arzikin Cikin Teku

Shirin NPA Na Kula Da Tashoshin Jiragen Ruwa A Dunkule Zai Bunkasa Tattalin Arzikin Cikin Teku

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.