Jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) sun bankado wasu da ke daukar nauyin wasu mutane zuwa kasar Saudiyya da nufin aikin hajji amma jigilar hodar iblis kawai suke yi musu zuwa kasar.
Kakakin hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, inda ya ce, an kama shugabannin da ke daukar nauyin mutanen ne a Kano.
- An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya
- Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Babafemi ya bayyana sunayen shugabannin da Abubakar Muhammad, Abdulhakeem Muhammed Tijjani, da Muhammad Aji Shugaba wadanda aka kama a ranakun Talata, 27 da Laraba 28 ga watan Mayun 2025 a Kano.
Ya bayyana kamen na su biyo bayan kama wasu alhazai biyu – Ibrahim Umar Mustapha da Muhammad Siraj Shifado a filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano, da ke Kano a ranar Litinin 26 ga watan Mayu.
An kama mutanen biyu ne a lokacin da ake tantance fasinjojin jirgin na Ethiopian Airline ET 940 da zai tafi zuwa Jedda, ta kasar Saudiyya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp