• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Cafke Wani Tubabban Dan Ta’adda Da Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
NDLEA Ta Cafke Wani Tubabban Dan Ta’adda Da Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA sun kama wani tubabben mayaki na kungiyar ta’addanci ta Boko Haram, Alayi Madu, da kuma wani sarki mai sarautar gargajiya na Kajola, dake kan iyaka tsakanin Ondo da jihar Edo, Ba’ale Akinola Adebayo, kan ta’ammuli da haramtattun kwayoyi.

Suna cikin mutane 37 da aka kama da sama da tan 2.2 na haramtattun kwayoyi da jami’an NDLEA suka kama a filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke Ikeja, Legas da kuma samame a jihohi 12 a cikin makon da ya gabata.

  • NDLEA Ta Kwace Kwaya Ta N1.5bn Da Cafke Mutum 1,078 Masu Safarar Kwaya A Kano.

Kakakin hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi, ya ce wannan nasara ce a wani bangare na ayyukan da ake yi na kawar da miyagun kwayoyi a fadin kasar nan.

Ya ce da sanyin safiyar Juma’a 10 ga watan Maris ne jami’an hukumar NDLEA suka kai wani samame a dajin Kajola da ke unguwar Kajola, inda suka lalata gonakin tabar wiwi guda uku masu girman hekta 39.801546.

An kama mai gonakin ne wanda ya yi ikirarin cewa shi ne Ba’ale na garin Kajola, Adebayo, mai shekaru 35 a gonar da misalin karfe 2:30 na dare, an kama shi tare da wasu mutane biyu da ake zargin ma’aikatansa ne: Arikuyeri Abdulrahman, dan shekara 23 da Habibu Ologun mai shekaru 25. an kama su ne a wata bukka da ke kusa da gonakin.

Labarai Masu Nasaba

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Hakazalika, wani matashi mai shekaru 26 Alayi Madu, wanda ya shafe shekaru 15 a kungiyar ta’addanci ta Boko Haram kafin ya mika wuya ga sojojin Nijeriya a shekarar 2021, jami’an NDLEA sun kama shi a ranar Alhamis, 9 ga watan Maris a hanyar Abuja zuwa Kaduna tare da haramtattun kwayoyi masu nauyin kilo 10, wanda ya ce ya saya ne a garin Ibadan na jihar Oyo zuwa Maiduguri, jihar Borno.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Cimma Yarjejeniya Tsakanin Saudiyya Da Iran A Beijing Ya Zo A Ba Zata

Next Post

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Zai Ingiza Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Related

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

22 minutes ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

1 hour ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

3 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

8 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

9 hours ago
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba
Labarai

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

10 hours ago
Next Post
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Zai Ingiza Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Zai Ingiza Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.