• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Cafke Wani Tubabban Dan Ta’adda Da Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi

by Sulaiman
3 years ago
NDLEA

Jami’an hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA sun kama wani tubabben mayaki na kungiyar ta’addanci ta Boko Haram, Alayi Madu, da kuma wani sarki mai sarautar gargajiya na Kajola, dake kan iyaka tsakanin Ondo da jihar Edo, Ba’ale Akinola Adebayo, kan ta’ammuli da haramtattun kwayoyi.

Suna cikin mutane 37 da aka kama da sama da tan 2.2 na haramtattun kwayoyi da jami’an NDLEA suka kama a filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke Ikeja, Legas da kuma samame a jihohi 12 a cikin makon da ya gabata.

  • NDLEA Ta Kwace Kwaya Ta N1.5bn Da Cafke Mutum 1,078 Masu Safarar Kwaya A Kano.

Kakakin hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi, ya ce wannan nasara ce a wani bangare na ayyukan da ake yi na kawar da miyagun kwayoyi a fadin kasar nan.

Ya ce da sanyin safiyar Juma’a 10 ga watan Maris ne jami’an hukumar NDLEA suka kai wani samame a dajin Kajola da ke unguwar Kajola, inda suka lalata gonakin tabar wiwi guda uku masu girman hekta 39.801546.

An kama mai gonakin ne wanda ya yi ikirarin cewa shi ne Ba’ale na garin Kajola, Adebayo, mai shekaru 35 a gonar da misalin karfe 2:30 na dare, an kama shi tare da wasu mutane biyu da ake zargin ma’aikatansa ne: Arikuyeri Abdulrahman, dan shekara 23 da Habibu Ologun mai shekaru 25. an kama su ne a wata bukka da ke kusa da gonakin.

LABARAI MASU NASABA

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

Hakazalika, wani matashi mai shekaru 26 Alayi Madu, wanda ya shafe shekaru 15 a kungiyar ta’addanci ta Boko Haram kafin ya mika wuya ga sojojin Nijeriya a shekarar 2021, jami’an NDLEA sun kama shi a ranar Alhamis, 9 ga watan Maris a hanyar Abuja zuwa Kaduna tare da haramtattun kwayoyi masu nauyin kilo 10, wanda ya ce ya saya ne a garin Ibadan na jihar Oyo zuwa Maiduguri, jihar Borno.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Gwamna Yusuf
Labarai

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
Sabbin Ministoci
Labarai

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Next Post
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Zai Ingiza Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Zai Ingiza Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.