• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Aikin Hajjin 2024

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
nahcon
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayyar Nijeriya da Kasar Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar gudanar da aikin hajjin 2024 a Jedda.

Ministan harkokin waje, Yusuf Tuggar shi ne ya jagoranci tawagar Nijeriya, yayin da ministan gudanar da aikin Hajji da Umara, Dakta Taufik Al-Rabiah ya jagoranci tawagar Saudiyya.

  • Shari’ar Kano: Kanawa Na Farin Ciki Kan Nasarar Abba A Kotun Koli
  • Shiriya, Ni’ima Da Gaskiyar Manzon Allah (SAW)

Mataimakiyar daraktan harkokin hukumar aikin hajjin Nijeriya, (NAHCON), Fatima Usara ta bayyana cewa tawagar ‘yan Nijeriya da suka halarci taron rattaba hannun ciki har da mukaddashin shugaban hukumar NAHCON, Jalal Arabi, sun bukaci karin wa’adi ga masu jigilar ‘yan Nijeriya tare da neman a kawo karshen matsalar da aka samu a lokacin hajjin bara a Mina.

Haka kuma gwamnatin tarayya ta bukaci ministan aikin hajji da umara na Kasar Saudiyya da ya ziyarci Nijeriya.

A nasa bangaren, Rabiah ya amince da kalubalen da aka samu a aikin hajjin bara a Mina, sannan ya bayar da tabbacin cewa ana kokarin inganta amfani da murabba’in fili mita miliyan 2 ga maniyyata miliyan biyu domin gudanar da aikin hajj a duk shekara.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Da yake amsa goron gayyatan zuwa Nijeriya nan ba da jimawa ba, Rabiah ya bayyana goyon bayan ma’aikatar wajen daukar matakan da suka dace na bai wa alhazai yanayi mai kyau domin gudanar da aikin hajji cikin natsuwa.

Haka kuma ya jaddada wa tawagar hukumar NAHCON sabon tsarin da aka fito da shi a harabar Masha’ir.

Dangane da bukatar da NAHCON ta shigar na samar da isasshen fili a Mina, Rabiah ya bayyana muhimmancin ajiye kudade da wuri domin samun wuraren da ya dace a Masha’ar, inda ya ce hakan ya sa ma’aikatarsa ta sabunta tsarin wanda ya riga zuwa shi za a fara la’akari da shi.

Ya bukaci NAHCON ta yi kokarin cin gajiyar wannan sabon tsari domin samun wuri a Masha’ir, kamar Kasar Saudiyya take kokarin guda da adalci wajen samun wuri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin HajjiKasar SaudiyyaNAHCON
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Da Sarki Letsie III Na Lesotho Sun Taya Juya Murnar Cika Shekaru 30 Da Dawo Hulda Tsakanin Kasashensu

Next Post

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Goyi Bayan Kasashen Yammacin Afirka Da Na Sahel

Related

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025
Labarai

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

6 hours ago
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna
Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

6 hours ago
Tinubu
Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

7 hours ago
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano
Labarai

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

8 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Labarai

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

9 hours ago
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

11 hours ago
Next Post
Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Goyi Bayan Kasashen Yammacin Afirka Da Na Sahel

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.