• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Aikin Hajjin 2024

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
nahcon

Gwamnatin tarayyar Nijeriya da Kasar Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar gudanar da aikin hajjin 2024 a Jedda.

Ministan harkokin waje, Yusuf Tuggar shi ne ya jagoranci tawagar Nijeriya, yayin da ministan gudanar da aikin Hajji da Umara, Dakta Taufik Al-Rabiah ya jagoranci tawagar Saudiyya.

  • Shari’ar Kano: Kanawa Na Farin Ciki Kan Nasarar Abba A Kotun Koli
  • Shiriya, Ni’ima Da Gaskiyar Manzon Allah (SAW)

Mataimakiyar daraktan harkokin hukumar aikin hajjin Nijeriya, (NAHCON), Fatima Usara ta bayyana cewa tawagar ‘yan Nijeriya da suka halarci taron rattaba hannun ciki har da mukaddashin shugaban hukumar NAHCON, Jalal Arabi, sun bukaci karin wa’adi ga masu jigilar ‘yan Nijeriya tare da neman a kawo karshen matsalar da aka samu a lokacin hajjin bara a Mina.

Haka kuma gwamnatin tarayya ta bukaci ministan aikin hajji da umara na Kasar Saudiyya da ya ziyarci Nijeriya.

A nasa bangaren, Rabiah ya amince da kalubalen da aka samu a aikin hajjin bara a Mina, sannan ya bayar da tabbacin cewa ana kokarin inganta amfani da murabba’in fili mita miliyan 2 ga maniyyata miliyan biyu domin gudanar da aikin hajj a duk shekara.

LABARAI MASU NASABA

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Da yake amsa goron gayyatan zuwa Nijeriya nan ba da jimawa ba, Rabiah ya bayyana goyon bayan ma’aikatar wajen daukar matakan da suka dace na bai wa alhazai yanayi mai kyau domin gudanar da aikin hajji cikin natsuwa.

Haka kuma ya jaddada wa tawagar hukumar NAHCON sabon tsarin da aka fito da shi a harabar Masha’ir.

Dangane da bukatar da NAHCON ta shigar na samar da isasshen fili a Mina, Rabiah ya bayyana muhimmancin ajiye kudade da wuri domin samun wuraren da ya dace a Masha’ar, inda ya ce hakan ya sa ma’aikatarsa ta sabunta tsarin wanda ya riga zuwa shi za a fara la’akari da shi.

Ya bukaci NAHCON ta yi kokarin cin gajiyar wannan sabon tsari domin samun wuri a Masha’ir, kamar Kasar Saudiyya take kokarin guda da adalci wajen samun wuri.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit
Labarai

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Manyan Labarai

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Next Post
Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Goyi Bayan Kasashen Yammacin Afirka Da Na Sahel

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.