• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Da NDLEA Reshen Bayelsa Sun Yi Ƙawancen Fatattakar Miyagun Ƙwayoyi Da Baƙin Haure

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
NDLEA

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), reshen Jihar Bayelsa ta yi ƙawance da takwararta ta yaƙi da sha da safarar miyagun ƙwayoyi ta NDLEA domin tabbatar da an fatattaki masu safarar ƙwaya da baƙin-haure a jihar.

Kwanturolan reshen Jihar Beyelsa na NIS, James Sunday ya amshi baƙoncin takwaransa na hukumar yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi (NDLEA), Barista Mathew Ewa a ofishinsa da ke Yenagoa, kan wannan sabon yunƙurin nasu.

Hukumar NIS ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar 7 ga watan Satumbar 2023, wanda jami’in hulɗa da jama’a na hukumar ya rattaba wa hannu.

Sanarwar ta ce lokacin wannan ziyarar, Kwamandan NDLEA ya bayyana cewa hukumarsa za ta ƙaddamar da shirin yaƙar ta’ammuli da miyagun ƙwayoyi da kakkave baƙin haure a Jihar Bayelsa, wanda za su gudanar tare da NIS, idan Shugaban hukumar NIS, Isah Idris Jere ya amince. Haka kuma shirin zai gudana ne tare da haɗin kan Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Douye Diri da sauren jami’an tsaro da ke Jihar Bayelsa.

Kwamandan ya ƙara da cewa za su yi aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran hukumomin tsaro a jihar wajen samun nasarar wannan shirin, wanda zai tsaftace jihar daga korarowar baƙin haure da masu ta’ammuli da miyagun ƙwaroyi ta hanyar bin ƙa’idogin ECOWAS idan da buƙatar hakan.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

NDLEA
Hoto na gaba daya tsakanin jami’an NIS da takwarorinsu na NDLEA reshen Jihar Bayelsa

Sanarwr ta ce hukumar NIS ce za ta jagoranci shirin a wani vangare na gudanar da aiki a lokaci bayan lokaci tare da tilasta wa mazauna jihar wajen bin doka ta yadda baƙin haure ba za su karya dokokin Nijeriya da na ECOWAS na shige da fice a tsakanin mambobin ƙasashen ba.

Ta ce idan aka samu duk wani mazaunin jihar da hannu wajen gudanar da kasuwancin da ya sava da dokokin Nijeriya da na ECOWAS tare da haɗa baki da baƙin haure a lokacin wannan shirin, za a hukunta shi daidai da laifinsa kamar yadda doka ta tanada.

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza
Labarai

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
Labarai

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Next Post
Matsalar Karancin Iskar Gas Na Addabar Turai Yayin Da Amurka Ke Kulla Makarkashiya

Matsalar Karancin Iskar Gas Na Addabar Turai Yayin Da Amurka Ke Kulla Makarkashiya

LABARAI MASU NASABA

Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.