• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Cafke Dillalan Makamai A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
NIS Ta Cafke Dillalan Makamai A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta ƙasa (NIS) ta ayyana cewa jami’anta sun cafke wasu mutane da ake zargin dillalan makamai ne a kan iyakar a Mfum da ke kan iyakar Nijeriya da Kamaru.

Garin Mfum wanda yake ƙaramar hukumar Ikom a Jihar Kuros Riba ya kasance cibiyar kasuwanci da ‘yan kasuwa na duniya ke yada zango yayin da suke safarar kayan abinci , man fetur da sauransu ta motoci zuwa ƙasar Kamaru .

Kwanturolan NIS mai kula da iyakar ƙasa ta Mfum, CI Ndubuisi Eneregbu ya yi bayanin cafke mutanen a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a ranar Lahadi .

 

  • EFCC Da NIS Za Su Yi Hadin Guiwa Kan Yaki Da Cin Hanci

Eneregbu ya bayyana cewa mutum uku da aka cafke sun haɗa da ‘Yan Nijeriya biyu da kuma wani baƙon-haure ɗan Kamaru wanda ya amsa cewa shi mamba ne na ƙungiyar ‘yan aware ta Ambazonia. An dai cafke su ne a kan babura ɗauke da bindigogi da albarusai .

Labarai Masu Nasaba

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

“An cafke mutanen da ake zargin ne ɗauke da wata jaka da aka sa ƙananan bindigogi biyu da albarusai guda uku da wasu kayan tsafi da kuma waya ƙirar TECNO.

“An miƙa mutanen da makaman da aka cafke su da su ga ofishin ‘yansanda na yankin Etung domin ci gaba da bincike.

Dangane da ƙoƙarin da NIS take yi na tsaurara tsaron iyakokin ƙasa kuwa, Kwanturolan ya ce hukumar ta ƙirƙiro da gudanar da taro a kai a kai tare da sarakunan dukkan garuruwan da ke kan iyaka domin samun nasara.

“Muna da kyakkyawar alaƙa a tsakaninmu da al’ummomin da ke iyakokin ƙasa . Mun gudanar da tarurruka daban-daban da al’ummomin tare da sauran humomin tsaro. A lokacin da na kama aiki a nan yankin , abin da na fara yi shi ne ziyarar dukkan sarakunan yankunan da ke ƙarƙashin kulawar ofishinmu.

“Abin da ya sa muka yi haka kuwa shi ne mun fahimci cewa akwai buƙatar kyautata alaƙa a tsakanin jami’an tsaro da al’ummomi. Babu wata hukumar tsaro da za ta bugi ƙirji ta ce za ta iya yaƙi da matsalar tsaro ita kaɗai ba tare da goyon bayan al’umma ba.

“A shirye muke mu tabbatar da tsaro a kan iyaka tare da tsaftace ta daga masu yin zangon ƙasa ga tattalin arziki. Idan ka leƙa Mbok ko Yahe da sauran garuruwa na iyaka duk za ka tarar da jami’anmu a wurin” ya bayyana.

  • https://leadership.ng/nis-redeploys-69-senior-officers/

 

Tuni dai Shugaban NIS , CGI Isah Idris Jere ya yaba wa jami’an da suka yi nasarar cafke mutanen kana ya hore su su ƙara azama domin tabbatar da sauke nauyin da ƙasa ta ɗora musu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kidayar ‘Yan Nijeriya Ta 2023: Shugaba Buhari Zai Bude Taron Masu Ruwa Da Tsaki

Next Post

Manta Tarihi Ya Sa Nijeriya Cikin Halin kaka-ni-ka-yi

Related

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

21 hours ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

2 weeks ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

3 weeks ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2

1 month ago
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

1 month ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

2 months ago
Next Post
Manta Tarihi Ya Sa Nijeriya Cikin Halin kaka-ni-ka-yi

Manta Tarihi Ya Sa Nijeriya Cikin Halin kaka-ni-ka-yi

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.