• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Tsawaita Ayyukan Ofisoshinta Zuwa Karshen Mako Domin Yi Wa Mutane Fasfo

Abin Zai Fara Daga 3 ga Disambar 2022 Zuwa 28 ga Janairun 2023

by Khalid Idris Doya
3 years ago
NIS

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), ta umarci wasu zababbun ofisoshin da ke yin fasfo a sassan kasar nan da su tsawaita ayyukan da suke gudanarwa na fasfo har zuwa ranakun karshen mako, don biyan bukatun tulin jama’a masu neman takardun fasfo da ke jibge a kasa.

Bayanin hakan na kunshe ne cikin sanarwar da jami’in watsa labarai na hukumar, Mista Tony Akuneme, ya fitar a Abuja.

  • 2023: Ba Ni Da Kudurin Mayar Legas Birnin Tarayyar Nijeriya – Tinubu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Hutun Mako 2 Ga Ma’aikata Maza Da Matansu Suka Haihu

A cewar Akuneme, Kwanturola-Janar na NIS, Idris Isa Jere, ne ya bayar da wannan umarnin, kuma ya amince da gaggauta kai kwanturolan sashen fasfo zuwa Jihohin Ekiti da Jigawa, sannan kuma wanda ke Ondo za a mayar da shi zuwa ofishin shiyya na hukumar da ke Ibadan.

A cewarsa, wannan sabon umarnin na daga cikin kokarin da ake son cimma wajen rage tulin bukatun fasfo da suka taru a tsakanin 2020 zuwa 2021 sakamakon kullen annobar Korona.

“Kwanturola-Janar, ya umarci ofisoshin a sassan kasar nan da ke da tulin bukatun fasfo da yawa a hannunsu da suke gudanar da ayyukansu har da ranukan Asabar.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

“Ana sa ran wannan aikin zai ke guduna duk ranar Asabar da zai fara aiki daga ranar 3 ga watan Disamban 2022 har zuwa ranar 28 ga watan Janairun 2023 daga karfe 10 na safe zuwa karfe 2 na rana,” a cewar sanarwar.

Kazalika, Kwanturola-Janar din, ya gargadi jami’an da ke kula da aikin samar da fasfo da su maida hankali wajen gudanar da ayyukansu yadda ya dace, ya gargadin dandana wa dukkanin jami’in da aka kama da saba ka’idar aiki.

Ana sa ran wannan mataki zai taimaka sosai wajen saukaka wa jama’a masu neman fasfo musamman a lokutan bukukuwan sabuwar shekara da na Kirsimeti.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
NIS
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Sha Alwashin Karfafa Hadin Gwiwar Kasarsa Da Rasha A Fannin Makamashi

Shugaban Kasar Sin Ya Sha Alwashin Karfafa Hadin Gwiwar Kasarsa Da Rasha A Fannin Makamashi

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
NIS

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.