• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Tsawaita Ayyukan Ofisoshinta Zuwa Karshen Mako Domin Yi Wa Mutane Fasfo

Abin Zai Fara Daga 3 ga Disambar 2022 Zuwa 28 ga Janairun 2023

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Tsawaita Ayyukan Ofisoshinta Zuwa Karshen Mako Domin Yi Wa Mutane Fasfo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), ta umarci wasu zababbun ofisoshin da ke yin fasfo a sassan kasar nan da su tsawaita ayyukan da suke gudanarwa na fasfo har zuwa ranakun karshen mako, don biyan bukatun tulin jama’a masu neman takardun fasfo da ke jibge a kasa.

Bayanin hakan na kunshe ne cikin sanarwar da jami’in watsa labarai na hukumar, Mista Tony Akuneme, ya fitar a Abuja.

  • 2023: Ba Ni Da Kudurin Mayar Legas Birnin Tarayyar Nijeriya – Tinubu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Hutun Mako 2 Ga Ma’aikata Maza Da Matansu Suka Haihu

A cewar Akuneme, Kwanturola-Janar na NIS, Idris Isa Jere, ne ya bayar da wannan umarnin, kuma ya amince da gaggauta kai kwanturolan sashen fasfo zuwa Jihohin Ekiti da Jigawa, sannan kuma wanda ke Ondo za a mayar da shi zuwa ofishin shiyya na hukumar da ke Ibadan.

A cewarsa, wannan sabon umarnin na daga cikin kokarin da ake son cimma wajen rage tulin bukatun fasfo da suka taru a tsakanin 2020 zuwa 2021 sakamakon kullen annobar Korona.

“Kwanturola-Janar, ya umarci ofisoshin a sassan kasar nan da ke da tulin bukatun fasfo da yawa a hannunsu da suke gudanar da ayyukansu har da ranukan Asabar.

Labarai Masu Nasaba

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

“Ana sa ran wannan aikin zai ke guduna duk ranar Asabar da zai fara aiki daga ranar 3 ga watan Disamban 2022 har zuwa ranar 28 ga watan Janairun 2023 daga karfe 10 na safe zuwa karfe 2 na rana,” a cewar sanarwar.

Kazalika, Kwanturola-Janar din, ya gargadi jami’an da ke kula da aikin samar da fasfo da su maida hankali wajen gudanar da ayyukansu yadda ya dace, ya gargadin dandana wa dukkanin jami’in da aka kama da saba ka’idar aiki.

Ana sa ran wannan mataki zai taimaka sosai wajen saukaka wa jama’a masu neman fasfo musamman a lokutan bukukuwan sabuwar shekara da na Kirsimeti.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FasfoJereNISUmarni
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Ba Ni Da Kudurin Mayar Legas Birnin Tarayyar Nijeriya – Tinubu

Next Post

Shugaban Kasar Sin Ya Sha Alwashin Karfafa Hadin Gwiwar Kasarsa Da Rasha A Fannin Makamashi

Related

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom
Labarai

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

51 minutes ago
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Manyan Labarai

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

2 hours ago
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

10 hours ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

11 hours ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

14 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

16 hours ago
Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Sha Alwashin Karfafa Hadin Gwiwar Kasarsa Da Rasha A Fannin Makamashi

Shugaban Kasar Sin Ya Sha Alwashin Karfafa Hadin Gwiwar Kasarsa Da Rasha A Fannin Makamashi

LABARAI MASU NASABA

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

July 29, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.