Jam’iyyar PDP a jihar Kebbi ta sanar da dakatar da wasu mambobinta kuma tsofaffin ministoci guda biyu Kabiru Tanimu Turaki, SAN da kuma Buhari Bala bisa zarginsu da ayyukan zagon kasa ga jam’iyyar a jihar.
Bayan tsofaffin Ministocin guda biyu, an dakatar da wasu mambobin jam’iyyar biyar bisa zarginsu da laifi iri daya da na tsofaffin ministocin.
A cikin wata sanarwa da sakataren jam’iyyar na jihar Abubakar Bawa Kalgo (Makaman Kalgo) ya raba wa manema labarai ranar Laraba a Birnin Kebbi, babban birnin jihar, ya ce, sauran mutum biyar din sun hada da; Haruna Saidu D.O., Sani Bawa Argungu, Ibrahim Abdullahi Manga, Bala Abdullahi Dole-Kaina, da Maryam Isah.
Kalgo ya bayyana cewa, dakatarwar ta fara aiki ne daga ranar 14 ga Maris, 2023 kamar yadda kwamitin zartarwa na jihar (SEC) da kuma dattawan jam’iyyar suka amince da hukuncin a jihar.
Sai dai, shugaban jam’iyyar na jihar, Usman Bello Suru, a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Birnin Kebbi, ya bayyana dakatarwar a matsayin abin jefarwa.
Ya ce abin da ya faru na cikin gida ne na jam’iyyar wanda nan ba da jimawa ba, komai zai daidaita kafin zaben gwamna da na ‘yan majalisar jiha da ke tafe da za a yi a ranar 18 ga Maris, 2023.