Babbar jam’iyyar adawa a Nijeriya PDP, ta sake zabar Amb. Umar El-Gash a matsayin shugabanta na jihar Yobe a zaɓen da aka gudanar a filin wasa na 27Agust da ke Damaturu.
Sabon shugaban yana sa ƙwarin gwuiwar cewa jam’iyyar za ta yi nasara a zaɓen 2027, yana mai cewa: “Mun shirya kwace mulki daga hannun APC a matakin shugaban ƙasa, da gwamnonin jihohi da na ‘yan majalisa.”
El-Gash ya zargi gwamnatin APC da taɓarɓarewar tsaro, da hauhawar farashin kayayyaki da matsalolin tattalin arziki, yana mai cewa: “Al’umma ba su iya samun abinci sau biyu a rana – suna jiran lokacin sauyi.”
Ya yaba wa shugaban jam’iyyar na riƙo Amb. Umar Iliya Damagum kan ƙoƙarinsa na haɗa kan jam’iyyar, yana mai cewa nasarar da PDP ta samu a zaɓen 2023 ta zo ne sakamakon haɗin kai.
A ƙarshe, sabon shugaban ya yi alƙawarin haɗa kan ‘yan jam’iyyar, da ƙarfafawa mata da matasa, da kafa tushe mai ƙarfi don ci gaban PDP a Yobe.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp