• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rana Ba Ta Karya: Habakar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Ba Mahassada Kunya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Rana Ba Ta Karya: Habakar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Ba Mahassada Kunya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan muka kalli halin da duniya ke ciki a natse, za mu ga cewa, illolin da ke tattare da tsauraran manufofin kudi na manyan tattalin arziki sun yi fice. Hadarin dake tattare da rashin hadin kai, babakare, rikice-rikice na yanki da siyasar kasa da kasa suna karuwa, kuma tattalin arzikin duniya yana kara tabarbarewa. Amma duk da wannan barazanar, tattalin arzikin Sin na nan da karfinsa daram. 

Kar a yaudare ku da labarun karya, Jimillar GDP na kasar Sin ya karu da kashi 5.2 cikin dari a shekara zuwa yuan tiriliyan 126.06 kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 17.71 a shekarar 2023, bisa ga bayanan da hukumar kididdiga ta kasar Sin (NBS) ta fitar. Sin ta ba da gudummawar sama da kashi 30 cikin 100 ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya tsawon shekaru a jere, tana matsayin gaba a cikin manyan kasashe masu karfin tattalin arziki a duniya kuma a matsayin babbar injin ci gaban tattalin arzikin duniya.

  • Amurka Ta Zama Babban Cikas Ga Dakile Yakin Gaza Bayan Da Ta Hau Kujerar Na Ki
  • Aleksandar Vučić: Yarjejeniyar Ciniki Cikin ‘Yanci A Tsakanin Sin Da Serbia Ta Bude Sabuwar Kofa Ga Bunkasuwar Serbia

Ci gaban tattalin arzikin kasar Sin ya samo asali ne sakamakon matakan da kasar ta dauka na daidaita fannonin tattalin arzikinta. A cikin shekaru 10 da suka gabata, kasar Sin ta aiwatar da matakan bude kofa ga waje da dama, da rage tsauraran matakan shigowa cikin kasar, da inganta yanayin da ya dace ga kamfanonin waje don zuba jari a kasar. Yadda kasar Sin ke kara ci gaba, haka take kara bude kofarta, ta kasance abin dogaro ga masu zuba jari a duniya. Aiwatar da dokar zuba jari ga kasashen ketare da daidaita ka’idojin tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa sun kara inganta tsarin zuba jarin waje.

Fiye da kashi 80 cikin 100 na kamfanonin ketare sun gamsu da yanayin kasuwancin kasar Sin a bara, yayin da sama da kashi 90 cikin 100 suka yi imanin cewa, kasuwar kasar Sin na da armashi, a cewar wani rahoto kan sakamakon binciken da majalisar bunkasa harkokin cinikayya ta kasa da kasa ta kasar Sin ta wallafa.

Idan aka yi la’akari da tarihi, bunkasuwar kasar Sin wani babban dalili ne na ci gaban dukkan bil’adama. Kasar Sin ta yau ba ta Sinawa kadai ba ce, ta zama kasar Sin ta duniya baki daya. Yayin da adadin ci gaban kasar Sin ya karu da kashi daya cikin dari, ci gaban sauran kasashe ya karu da kashi 0.3 cikin dari, bisa ga binciken IMF. Kasar Sin na ci gaba da himmatuwa wajen inganta yanayin kasuwanci ga masu zuba jari, tana kara kaimi ga farfadowar tattalin arzikin duniya, yayin da mahassada ke jiran labarin rugujewar tattalin arzikinta. (Muhammed Yahaya)

Labarai Masu Nasaba

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Dauda Ya Sanar Da Ɗaukar Ma’aikata Da Samar Da Garejin Tireloli A Zamfara

Next Post

Dalibai 180 Sun Kammala Digiri Da Daraja Ta Daya A Jami’ar Bayero, Kano

Related

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

1 hour ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

3 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

4 hours ago
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

15 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

20 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

20 hours ago
Next Post
BUK

Dalibai 180 Sun Kammala Digiri Da Daraja Ta Daya A Jami’ar Bayero, Kano

LABARAI MASU NASABA

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.