• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rana Ba Ta Karya: Habakar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Ba Mahassada Kunya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Rana Ba Ta Karya: Habakar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Ba Mahassada Kunya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan muka kalli halin da duniya ke ciki a natse, za mu ga cewa, illolin da ke tattare da tsauraran manufofin kudi na manyan tattalin arziki sun yi fice. Hadarin dake tattare da rashin hadin kai, babakare, rikice-rikice na yanki da siyasar kasa da kasa suna karuwa, kuma tattalin arzikin duniya yana kara tabarbarewa. Amma duk da wannan barazanar, tattalin arzikin Sin na nan da karfinsa daram. 

Kar a yaudare ku da labarun karya, Jimillar GDP na kasar Sin ya karu da kashi 5.2 cikin dari a shekara zuwa yuan tiriliyan 126.06 kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 17.71 a shekarar 2023, bisa ga bayanan da hukumar kididdiga ta kasar Sin (NBS) ta fitar. Sin ta ba da gudummawar sama da kashi 30 cikin 100 ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya tsawon shekaru a jere, tana matsayin gaba a cikin manyan kasashe masu karfin tattalin arziki a duniya kuma a matsayin babbar injin ci gaban tattalin arzikin duniya.

  • Amurka Ta Zama Babban Cikas Ga Dakile Yakin Gaza Bayan Da Ta Hau Kujerar Na Ki
  • Aleksandar Vučić: Yarjejeniyar Ciniki Cikin ‘Yanci A Tsakanin Sin Da Serbia Ta Bude Sabuwar Kofa Ga Bunkasuwar Serbia

Ci gaban tattalin arzikin kasar Sin ya samo asali ne sakamakon matakan da kasar ta dauka na daidaita fannonin tattalin arzikinta. A cikin shekaru 10 da suka gabata, kasar Sin ta aiwatar da matakan bude kofa ga waje da dama, da rage tsauraran matakan shigowa cikin kasar, da inganta yanayin da ya dace ga kamfanonin waje don zuba jari a kasar. Yadda kasar Sin ke kara ci gaba, haka take kara bude kofarta, ta kasance abin dogaro ga masu zuba jari a duniya. Aiwatar da dokar zuba jari ga kasashen ketare da daidaita ka’idojin tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa sun kara inganta tsarin zuba jarin waje.

Fiye da kashi 80 cikin 100 na kamfanonin ketare sun gamsu da yanayin kasuwancin kasar Sin a bara, yayin da sama da kashi 90 cikin 100 suka yi imanin cewa, kasuwar kasar Sin na da armashi, a cewar wani rahoto kan sakamakon binciken da majalisar bunkasa harkokin cinikayya ta kasa da kasa ta kasar Sin ta wallafa.

Idan aka yi la’akari da tarihi, bunkasuwar kasar Sin wani babban dalili ne na ci gaban dukkan bil’adama. Kasar Sin ta yau ba ta Sinawa kadai ba ce, ta zama kasar Sin ta duniya baki daya. Yayin da adadin ci gaban kasar Sin ya karu da kashi daya cikin dari, ci gaban sauran kasashe ya karu da kashi 0.3 cikin dari, bisa ga binciken IMF. Kasar Sin na ci gaba da himmatuwa wajen inganta yanayin kasuwanci ga masu zuba jari, tana kara kaimi ga farfadowar tattalin arzikin duniya, yayin da mahassada ke jiran labarin rugujewar tattalin arzikinta. (Muhammed Yahaya)

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Dauda Ya Sanar Da Ɗaukar Ma’aikata Da Samar Da Garejin Tireloli A Zamfara

Next Post

Dalibai 180 Sun Kammala Digiri Da Daraja Ta Daya A Jami’ar Bayero, Kano

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

13 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

14 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

15 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

16 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

17 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
BUK

Dalibai 180 Sun Kammala Digiri Da Daraja Ta Daya A Jami’ar Bayero, Kano

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.