Shugaban Æ™ungiyar gwamnonin Nijeriya (NGF), kuma gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya jagoranci takwarorinsa wajen ziyarar ta’aziyyar ga mataimakin shugaban Æ™asa, Kashim Shettima, bayan dawowarsa birnin tarayya Abuja, a ranar Laraba.
Gwamnonin, sun yi addu’ar Allah ya jiƙan surukar mataimakin shugaban ƙasa, marigayiya Hajiya Maryam Albishir, ya kuma bai wa iyalanta haƙurin jure rashinta.
- Nijeriya Ta Aike Dakaru 177 Guinea Bissau Don Wanzar Da Zaman Lafiya
- Philippines Ta Zama Makamin Sarrafawa Ga Amurka
Da yake godiya da ziyarar, mataimakin shugaban Æ™asar, ya nuna jin daÉ—insa kan ta’aziyar da gwamnonin suka kawo da yadda suka nuna tausayi da goyon baya gare shi.
Shettima ya yaba da haɗin kan Gwamnonin da Gwamnatin Tarayya ya kuma yi kira da a ƙara ba da hadin kai da goyon baya ga Shugaba Bola Tinubu, domin cimma manufofinsa da na ƙasa baki daya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp