• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rukunin farko na ‘yan Nijeriya da aka kwaso daga kasar Sudan sakamakon yakin da kasar ke ciki sun iso Nijeriya inda suka hadu da ‘yan uwansu da jami’an Gwamnati cikin farin ciki da annashuwa.

Daliban da aka kwaso ta hanyar amfani da filin Jirgin kasar Egypt, sun sauka a Abuja ne da misalin karfe 11:30 na daren ranar Laraba kamar yadda ma’aikatar kula da harkokin cikin gida ta sanar.

  • Rukunin Farko Na Sinawa Da Aka Kwashe Daga Sudan Ya Sauka A Birnin Beijing

‘Yan Nijeriyan wadanda suka sauka a filin Jirgin kasa da kasa ta Nnamdi Azikiwe a cikin jirgi mallakin sojojin saman Nijeriya da na Air Peace.

A lokacin da take karbar mutanen a filin jirgin, Darakta sashin kula da ‘yan gudun hijira ta hukumar kula da da ‘yan gudun hijira da kaura kasa, Misis Catherine Udida, ta ce jirgin Airforce C130 ne ya kwashe mutane 94, yayin da Air Peace ya kwashe mutane 282

Shugaban ‘yan Nijeriya mazauna kasashen waje, (NiDCOM), Mrs. Abike Dabiri-Erewa, ta ce, an samu gagarumar tarba cikin murna ga ‘yan kasan lura da halin da suka samu kansu da yadda aka yi ta jin labarin suke ciki a can kasar ta Sudan.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Ministar Jin Kai, Hajiya Sadiya Umar Farouq, babban Sakataren ma’aikatar, Dr Nasir Sani-Gwarzo, darakta Janar na hukumar NEMA, Mustapha Habib, da jami’an tsaro hadi da wasu daga cikin iyalan dalbannne suka tarbesu a filin Jirgin.

Majiyoyi sun shaida cewar ‘yan Nijeriyan da suka dawo sun Yi murna matuka tare da iyalansu bisa yadda suka tsinci kansu a cikin kasar Sudan na mawuyacin hali da wahalar da suka sha wajen fitowa daga Sudan zuwa iyakar kasar.

Rikicin kasar Sudan dai zuwa yanzu ya lakume kusan rayuka 600 da tilasta wa dubbai kaura daga muhallansu sannan kasashen da dama suna ta kwashe ‘yan kasuwarsu da ke rayuwa a can.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsare-Tsare Ga Ma’aikata: Gwamnonin Bauchi Da Gombe Sun Samu Babbar Lambar Yabo Daga Kungiyar Kwadago Ta TUC

Next Post

Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Yaba Wa ‘Yan Jarida Bisa Yada Ayyukan Hukumar

Related

‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

58 minutes ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

2 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

4 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

4 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

8 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

9 hours ago
Next Post
NIS

Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Yaba Wa ‘Yan Jarida Bisa Yada Ayyukan Hukumar

LABARAI MASU NASABA

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.