• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar PLA Ta Kasar Sin Ta Kammala Atisayen Hadin Gwiwa Na Kwanan Nan

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
PLA

Rundunar sojin ’yantar da al’ummar kasar Sin(PLA) ta yankin gabashi, ta yi nasarar kammala dukkan ayyukan da aka tsara na atisayen hadin gwiwa da aka gudanar a ranakun Talata da Laraba, kamar yadda mai magana da yawun rundunar da ta yi atisayen, babban kanar Shi Yi ya bayyana.

Shi Yi ya ce, dakarun rundunar atisayen na ci gaba da kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana, kuma za su ci gaba da karfafa shirye-shiryen yaki tare da samun kwakkwaran horon soji don dakile duk wani yunkurin ballewa na neman ’yancin kai na Taiwan.

  • ‘Yansanda Sun Gayyaci Shamakin Kano Kan Zargin Karya Dokar Haramta Hawan Sallah
  • Janar Tsiga Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Bayan Shafe Kwanaki 56 A Hannun ‘Yan Bindiga 

An kuma bayar da rahoton cewa, Amurka, da Tarayyar Turai, da Japan da sauransu sun yi tsokaci kan atisayen na hadin gwiwa da sojojin ’yantar da al’ummar kasar Sin suka gudanar a kusa da tsibirin Taiwan a ranar 1 ga watan Afrilu, inda suka zargi kasar Sin da yin barazanar da ba ta dace ba, da karin matsin lambar matakin soji a tsibirin Taiwan ba tare da wasu kwararan dalilai ba.

Dangane da haka, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun ya bayyana a taron manema labarun da aka saba yi a-kai-a-kai, da ya gudana yau 2 ga watan Afrilu cewa, batun Taiwan tsantsar lamari ne na cikin gidan kasar Sin kurum, kuma ba a yarda da tsoma bakin ’yan-ba-ni-na-iya daga waje ba.

Kana ya ce, abun da ke kawo cikas ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a mashigin tekun Taiwan shi ne hadin baki da goyon bayan ayyukan masu fafutikar ballewar Taiwan daga wasu rundunoni na waje. Kuma idan har da gaske ne kasashe da kungiyoyin da abun ya shafa suna fatan samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a mashigin tekun Taiwan, kamata ya yi su bi tsarin kasa da kasa da aka aminta da shi wajen kiyaye ka’idar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, da kiyaye alkawuran siyasa da aka yi wa kasar Sin, da mutunta ikon mallakar kasa da ’yancin kan Sin da yankunanta, da kuma nuna adawa da duk wani nau’i na “’yancin kan Taiwan.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC
Daga Birnin Sin

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Mun Rage Tasirin ‘Yan Bindiga A Kebbi Da Zamfara - Sojoji

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.