• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar PLA Ta Kasar Sin Ta Kammala Atisayen Hadin Gwiwa Na Kwanan Nan

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Rundunar PLA Ta Kasar Sin Ta Kammala Atisayen Hadin Gwiwa Na Kwanan Nan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar sojin ’yantar da al’ummar kasar Sin(PLA) ta yankin gabashi, ta yi nasarar kammala dukkan ayyukan da aka tsara na atisayen hadin gwiwa da aka gudanar a ranakun Talata da Laraba, kamar yadda mai magana da yawun rundunar da ta yi atisayen, babban kanar Shi Yi ya bayyana.

Shi Yi ya ce, dakarun rundunar atisayen na ci gaba da kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana, kuma za su ci gaba da karfafa shirye-shiryen yaki tare da samun kwakkwaran horon soji don dakile duk wani yunkurin ballewa na neman ’yancin kai na Taiwan.

  • ‘Yansanda Sun Gayyaci Shamakin Kano Kan Zargin Karya Dokar Haramta Hawan Sallah
  • Janar Tsiga Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Bayan Shafe Kwanaki 56 A Hannun ‘Yan Bindiga 

An kuma bayar da rahoton cewa, Amurka, da Tarayyar Turai, da Japan da sauransu sun yi tsokaci kan atisayen na hadin gwiwa da sojojin ’yantar da al’ummar kasar Sin suka gudanar a kusa da tsibirin Taiwan a ranar 1 ga watan Afrilu, inda suka zargi kasar Sin da yin barazanar da ba ta dace ba, da karin matsin lambar matakin soji a tsibirin Taiwan ba tare da wasu kwararan dalilai ba.

Dangane da haka, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun ya bayyana a taron manema labarun da aka saba yi a-kai-a-kai, da ya gudana yau 2 ga watan Afrilu cewa, batun Taiwan tsantsar lamari ne na cikin gidan kasar Sin kurum, kuma ba a yarda da tsoma bakin ’yan-ba-ni-na-iya daga waje ba.

Kana ya ce, abun da ke kawo cikas ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a mashigin tekun Taiwan shi ne hadin baki da goyon bayan ayyukan masu fafutikar ballewar Taiwan daga wasu rundunoni na waje. Kuma idan har da gaske ne kasashe da kungiyoyin da abun ya shafa suna fatan samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a mashigin tekun Taiwan, kamata ya yi su bi tsarin kasa da kasa da aka aminta da shi wajen kiyaye ka’idar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, da kiyaye alkawuran siyasa da aka yi wa kasar Sin, da mutunta ikon mallakar kasa da ’yancin kan Sin da yankunanta, da kuma nuna adawa da duk wani nau’i na “’yancin kan Taiwan.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Gayyaci Shamakin Kano Kan Zargin Karya Dokar Haramta Hawan Sallah

Next Post

Mun Rage Tasirin ‘Yan Bindiga A Kebbi Da Zamfara – Sojoji

Related

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

2 hours ago
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

3 hours ago
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

22 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

23 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

23 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

1 day ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Mun Rage Tasirin ‘Yan Bindiga A Kebbi Da Zamfara - Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

June 8, 2025
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

June 8, 2025
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

June 8, 2025
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

June 8, 2025
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.