• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

by Zubairu M Lawal and Sulaiman
4 weeks ago
Makamai

Kwamishinan ‘Yansandan jihar Nasarawa CP. Shattima Muhammad ya bayyanawa manema labarai rawar da Rundunar ‘yansandan jihar suka taka wajen kama masu aikata miyagun laifuka. Kwamishinan ya bayyana cewa rundunar ta kama mutum 9 tare da kwato harsasai 4,264 a wasu ayyukan sintiri da aka gudanar a ƙananan hukumomi 13 na jihar.

 

CP Shattima Mohammed, ne ya bayyana hakan a taron manema labarai da aka gudanar a ofishin rundunar a Lafia, babban birnin jihar.

  • Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024
  • Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Yayin da yake bayyana alkaluman a babban birnin jihar, Lafia, CP Mohammed ya ce, “A ranar 7 ga Satumba, 2025, da misalin ƙarfe 6:30 na yamma, bisa sahihan bayanan sirri cewa, wasu da ake zargin masu safarar makamai daga jihar Benuwe sun isa wani daji da ke iyakar Kadarko, a karamar hukumar Keana , suna sauke makamai da harsasai domin rarraba wa abokan harkarsu.

 

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

“Da samun rahoton, babban jami’in ‘yansanda na yankin, ya jagoranci tawagar jami’an ‘yansanda kai tsaye zuwa wurin.

 

“Da suka hango jami’anmu, sai suka ajiye kayan suka tsere cikin daji. Binciken wurin ya haifar da gano makaman nan: bindigogi AK-49 guda huɗu, bindigogi AK-47 guda uku, bindiga G3 guda ɗaya, bindiga ƙarama (Sub-Machine Gun) guda ɗaya, mujallu harsasai guda goma sha ɗaya, harsasai 7.62mm guda 4,046, harsasai 5.5mm guda goma sha ɗaya, harsasai 38mm guda 132, da harsashi guda 75.”

 

CP Mohammed ya ƙara da cewa, a wani samame da aka yi ranar 6 ga Satumba, 2025, bisa bayanan sirri, an kama wani mutum mai suna John Paul daga Abuja a tashar motar Akwanga-Wamba yayin da yake kan hanyarsa zuwa Abuja. Da aka binciki jikinsa, an gano bindigogi biyar kirar gida, kuma wanda ake zargin ya bayyana cewa da akwai abokan harkansa. Tuni ‘yansanda suka bazama nimansu.

 

Haka kuma da misalin ƙarfe 3:00 na dare jami’an da ke ofishin ‘E’ Division a Shabu, cikin Lafia, sun kama manyan masu ƙera bindigogi biyu, James Philip da Alpha Philip, dukkansu maza ne daga unguwar Faferuwa, Lafia.

 

“Bincike ya kai ga kama manyan masu saye da sai da bindigogin da aka kirar gida , waɗanda suka haɗa da Usman Abubakar daga Shendam Road, Lafia Yakubu Danladi daga Mararaba Akunza, Lafia; Usman Kasimu wanda aka fi sani da Bobo daga Bukan Sidi, Lafia; da Abdullahi Adamu daga Bukan Sidi, Lafia.

 

Abubuwan da aka kwato daga hannunsu sun haɗa da: bindigogi dogaye guda 13, bindigogi ƙanana guda 10, bindiga Revolver guda ɗaya, takuba guda uku, Rigunan sanye na ƴan sanda guda uku da hulun su, injinan ƙera bindiga guda uku da kayan aiki,

 

Yayin da yake yabawa jajircewar jami’an sa, CP Shattima Mohammed ya tabbatar wa mazauna jihar cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kawar da miyagun mutane a Nasarawa.

 

Ya ce, “Ina kira ga kowa ya kasance mai lura, mai bin doka, kuma ya rika bayar da bayanai ga Rundunar yan sanda.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Labarai

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana'antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.