• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabo Ahmad Kafin-Maiyaki: Abubuwan Da Ba Za Mu Taba Mantawa Da Su Ba

Inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un.

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Sabo Ahmad Kafin-Maiyaki: Abubuwan Da Ba Za Mu Taba Mantawa Da Su Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rasuwar Malam Sabo Ahmad Kafinmaiyaki gibi ne mai wuyar cikewa a cikin al’umma. A iya zaman da na yi shi na karu da abubuwa da dama musamman a fannin aikin jarida.

A lokacin da yana Editan LEADERSHIP A Yau Lahadi, Malam ya kan zaunar da ni kamar abokinsa mu tattauna akan abin da ya shafi aiki da zamantakewa, a irin wannan zama da mu kan yi da shi yake bani labarin dangantarsa da Jihar Kano, inda ya ce ai shi dan asalin Jihar Kano ne, a unguwar Yakasai dake yankin Karamara Hukumar Birnin da kewaye wato Kano Municipal, har ma yake ce min iyayensu su ne asalin masu unguwar Yakasai, kuma har yanzu idan ya je Kano ba ya fara zuwa ko ina sai Yakasai ya sadar da zumunci koda kuwa bai wani abin ne ya kai shi daban.

  • Cire Tallafin Mai Ya Dace, Amma A Gaggauta Saukaka Wa Al’umma
  • Hukumar GEIDCO Ta Zayyana Ayyuka Da Za A Samar A Afirka

Kafin ya zama Editan Jaridar LEADERSHIP a sashen Hausa, Malam Sabo ya kafa jarida tasa ta kansa mai suna Aljazira, wacce shi kadai ne yake gudanar da ita da aljihunsa da tunaninsa da kuma sauran wadanda suke taimaka masa. Ganin wannan hazaka tasa ta sa aka neme shi domin ya ba da gudunmawa a LEADERSHIP, a lokacin da kamfanin ya bude sashen Hausa da za ta rika fita a kullum wato LEADERSHIP A Yau, karkashin jagorancin marigayi Sam Nda Isiah, wanda kuma shi ya kafa kamfanin, wanda Editocin jaridar suka hada da Sulaiman Bala Idris a matsayin Editan jaridar da za ta rika fita kullum, wanda daga karshe ya samu ci gaba izuwa daraktan sashen Hausa, wanda a yanzu shi ne Sakataren Yada Labarai na zababben Gwamnan Zamfara.

Sai kuma Malam Abdurrazak Yahuza Jere, a matsayin Editan ranar Juma’a, Mubarak Umar Abubakar, shi ne Editan ranar Asabar, wanda shima daga baya ya samu karin girma zuwan Draktan sashen Hausa na jaridar, kafin daga bisani Sulaiman Bala Idris ya zama daraktan sashen.

A bayan da Mubarak ya samu ci gaba ne sai aka nemo Malam Sabo domin ya maye gurbinsa a matsayin Editan jaridar ta ranar Asabar.

Labarai Masu Nasaba

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

Daga baya kuma kamfanin ya sauya tunaninsa bayan rasuwar marigayi Sam inda aka sake dawo da jaridar asalin matsayinta na da wato LEADERSHIP Hausa.

Wannan canji da aka yi, ya sanya a rushe dukkanin Editocin guda uku, bayan da maidakin marigayi Sam wato Mis Zainab Nda Isiah ta karbi jan ragamar kamfanin, wanda a halin yanzu Malam Abdurrazak Yahura Jere shi ne Babban Edita a sashen LEDAERSHIP Hausa.

Abin da ya sa na kawo wannan dan gajeren tarihin domin mu dubi irin hakuri na Malam Sabo, wanda yana matsayin Edita aka dawo da shi matsayin shugaban sashen fassara da bin diddigi, amma hakan bai sa ya ki karbar matsayin ba duk yana kasan wancan matsayi nasa na farko, da hakan ya ci gaba da biyayya gami da karbar umarni daga babban Edita Abdurrarak Yahuza Jere, haziki kuma jajirtacce.

Zan iya cewa Malam Sabo yana daga cikin mutanen da na tabbatar irinsu a cikin al’umma daban ne. Sannan shi mutum ne mai amana da gaskiya, ga kawaici, in dai ana zaune a wurin aiki duk irin hirar da ake yi idan har ba ta shafe shi ba, zai yi wuya ka ji ya tsoma baki.

A duk lokacin da zai tafi sayo abinncin dare ko rana ko na safiya sai ya tambayi kowa shin akwai mai sako? Idan akwai mai sako haka za a tara masa kudin abincin mafi aksarinmu duk ya grime mu amma haka zai karbi kudinmu ya tafi ya sayo, ka ganshi da abinci da yawa a hannunsa. Muma mu kan je mu sayo, amma dai abin dubawa shi ne yadda yara irinmu da ya sa ya grime mu amma ba ya kyashin ya karbi sakonmu ya amso mana wani abin aike, a nan kuma rashin girman kai yake nunawa.

To a irin wannan sayo abincin ne ya tafi Utako ya sayo wa abokan aiki abin muda baki, ya yanke jiki ya fadi, wanda tun da ya yi wannan faduwa Allah bai kaddara masa tashi ba.

Kusan in ce wannan shi ne kadan daga abin da zan iya tunawa a halayyarsa a zaman da na yi da shi, amma idan masu karatun na bibiyar shafin bayan jaridar nan za su ga sauran abokan aiki na ci gaba da fadar halayensa.

Malam Sabo ya yi aiki a tsakanin zakakuran Editoci matasa.

Muna addu’ar Allah ya ji kansa da rahma ya kyautata makwancinsa ya saka masa da mafificin alheri, ya shiryi bayansa, ya ba wa iyaye iyalai, ‘yan uwa da abokan arzikinsa da mu abokan aikinsa hakurin juriyar wannan babban rashi.

Allah ya jikan dukkanin al’ummar Musulmi da suka riga mu gidan gaskiya ya bamu sa’ar tad da su ya sa mu yi kyakkyawan karshe.

Idris Aliyu Daudawa: Allahu akbar, Allahu akbar, Kullu nafsin za’ikatul maut,

Wannan al’amarin haka yake daukacin duk mai rai wata rana shi ma zai koma ga mahaliccinsa da zarar lokacin komawarsa ya yi, haka abin zai kasance babu karin wani lokaci ko da kuwa dakika daya ce.

Al’amarin rayuwa ke da haka sai dai babbar fatan da kowa yake kullum shi ne ya cika da imani wato kalmar shahada wacce ba karamar nasara bace mutum ya cika da ita.

Wannan rubutu mun yi shi ne saboda rashin abokin aikinmu Sabo Ahmed Kafin Maiyaki, da Allah ya yi ma sa rasuwa yau kwana 22 da suka gabata ke nan, bayan ya yi fama da rashin lafiya a inda aka kwantar da shi a Asibitin Sabana dake Zariya.

Ya rage saura kwana biyu a yi karamar Sallah wato ranar Laraba kenan bayan da aka kammala bin diddigi na dukkan shafukan Jaridar LEADERSHIP Hausa kafin a kai ga wallafa ta, lamarin ya faru a cikin watan azumin Ramadan, kamar yadda muka saba yi mu kan je sayo sayen abincin buda baki tare da shi muka tafi muna tafiya muna ta hira ganin ga karamar Sallah ta matso domin  a lokacin sauran kwana biyu, saboda an yi ta ranar Juma’a ne, a nan wurin sayen abincin ne muna tsaye ya yanke jiki ya fadi.

Ganin haka ta faru tun da lokacin hankalina ya tashi, nan da nan sai na kira Malam Bello Hamza da Rabi’u Ali Indabawa suka zo daga ofis inda muka dauke shi tare da wani yaro Zarahaddini zuwa wani asibiti domin bashi agajin gaggawa, inda ya kwana a wannan asibiti.

Washegari ranar Alhamis Malam Bello ya sanya shi a mota aka tafi da shi Zariya inda ba a zame ko ina ba sai asibiti.

A tsawon shekara shida da muka kasance da marigayi Malam Sabo, na sani mutum ne wanda yake da matukar hakuri da kawaici kunya da yakana domin kuwa zai yi matukar wuya ya ka ga abin da zai bata masa rai, a ko da yaushe ya kan so ya rika ba wa mutum shawara, shawararsa ba ta wuce mutum ya rika yin hakuri da al’amuran duniya saboda wata rana ai sai labari.

Mutum ne da ba shi da girman kai saboda duk yadda kake zai saurare ka koda wata shawara ce daga wurinsa zai baka wadda idan ka yi amfani da ita ba za ka yi nadama ba.

Akwai shi da kokarin karfafa sada zumunci

Lokaci zuwa lokaci yana tafiya kafin Maiyaki wajen ‘yan uwansa ko kuma taron kungiyarsu ta tsofaffin dalibai na makarantar Sakandare ta Kafin Maiyaki. Ya kan je ne karshen wata ko bayan ‘yan makonni.

Ta bangaren aiki ana iya cewa hazikin ne saboda ilmin da yake da shi a fannin Turanci da Hausa wadda ko ta wanne fanni in ka nemi shawara shi zai baka musamman ma idan yana magana kana sauraren sa kamar yadda ya dace, gaskiya ba karamin rashi aka yi ba, daga iyalansa da kuma sauran ‘yan’uwansa da abokan huldarsa.

Fatan kowa shi ne Allah ya yafe masa kura- kurensa da ya aikata, mu kuma idan tamu ta zo mu cika da imani. Ba ni kadai ba daukacin sauran ‘yan’uwa ma’aikatan bangaren LEADERSHIP Hausa sun karu matuka da basirarsa ta bangaren Hausa da aikin Jaridar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ahmad SaboEditaLeadership HausaTa'aziyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

DA DUMI-DUMI: DSS ta Karyata Cafke Gwamnan CBN Da Aka Dakatar

Next Post

Sojoji Sun Yi Nasarar Kashe ‘Yan Ta’adda 6 Da Kwato Makamai Da Dama A Kaduna

Related

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA
Manyan Labarai

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

13 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

19 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

1 day ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

1 day ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

1 day ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

2 days ago
Next Post
Sojoji Sun Yi Nasarar Kashe ‘Yan Ta’adda 6 Da Kwato Makamai Da Dama A Kaduna

Sojoji Sun Yi Nasarar Kashe ‘Yan Ta’adda 6 Da Kwato Makamai Da Dama A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

May 16, 2025
Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

May 16, 2025
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

May 16, 2025
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

May 16, 2025
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

May 16, 2025
Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.