• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Jakadan Nijar A Rasha Ya Mika Wasikar Kama Aiki Ga Shugaba Putin

by Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Sabon Jakadan Nijar A Rasha Ya Mika Wasikar Kama Aiki Ga Shugaba Putin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasar Rasha Bladimir Putin ya karbi wasikar jakadanci ta sabon jakadan Nijar a kasar Rasha a fadar Kremlin dake Birnin Moscou.

 

Gwamnatin Nijar, a yayin wani zaman taron ministoci na ranar 15 ga watan Mayun shekarar 2024, ta amince da nada Janar Abdou Sidikou Issa a wannan muhimmin matsayi, wanda kuma hakan ya nuna cewa, tsohon shugaban rundunar sojojin Nijar, Janar Abdou Sidikou Issa zai wakilci bangaren diplomasiyyar Nijar a kasar Rasha.

  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje
  • Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

Inda ya mika takardar jakadancinsa ga shugaban Kasar Rasha Bladimir Putin a Nuwamban shekarar 2024.

 

Labarai Masu Nasaba

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Shi dai tsohon manjo-janar din sojojin Nijar, Abdou Sidikou Issa, sananne ne a fagen siyasar Nijar, kuma mutum ne mai son aiki, da ya taka muhimmiyar rawa a lokacin juyin mulkin ranar 23 ga watan Yulin shekarar 2023.

 

Kazalika a 2024, ministan sadarwa Sidi Mohamed Raliou ya gana da dukkan wakilan gidajen rediyo, talabijin da jaridu na kasashen waje dake aiki a Nijar, ganawar da ta gudana a ofishin ma’aikatar sadarwa dake Birnin Yamai.

 

Wannan ganawa irin ta ta farko, ta kasance wani tsarin tattaunawa, da yin musaya kan batutuwa da dama da suka shafi tsinkayen shugaban kwamitin ceton kasa da kuma daidaita matsayin wakilai da aikinsu a Nijar.

 

Ministan sadarwa ya bukaci ganin goyon bayan wakilan kafofin watsa labarai na kasashen waje dake Nijar game da hangen shugaban kwamitin ceton kasa na CNSP Abdourahamane Tiani da ya rataya kan zaman jituwa tsakanin al’ummar kasa, tsaro da kuma mulki na-gari.

 

Haka zalika, minista Sidi Mohamed Raliou ya ja hankalin wadannan ‘yan Nijar dake ma kafafen sadarwa na kasashen waje aiki a Nijar, da su kasance masu kishin kasa, da su sanya moriyar kasarsu a gaba, da kuma fifita ci gaban kasarsu.

 

A nasu bangare, mahalarta wannan ganawa sun nuna jin dadi da gamsuwarsu game da wannan tunani na ma’aikatar sadarwa bisa ga shirya wannan haduwa.

 

Haka kuma, sun yi amfani da wannan dama, domin bayyanawa minista Sidi Mohamed Raliou, matsalolin da suke fuskanta game da neman labarai daga wajen hukumomi, da kuma fatan ganin an daidaita wadannan matsaloli.

 

Daga karshe, minista Sidi Mohamed Raliou, ya tabbatarwa wadannan ‘yan jarida niyyarsa na rakiyarsu da kuma kasancewa mai saurarensu a kowane lokaci, tare da yin musanya kan batutuwan da za su taimaka musu tafiyar da aikinsu cikin sauki kuma cikin girmama ka’idodin aikin jarida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babbar Majalisar Dokokin Kasar Sin Ta Yi Allah Wadai Da Abin Da Ake Kira Dokar Yankunan Teku Na Philippines

Next Post

Shanghai: An Gudanar Da Taron Majalisar Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’ummar Sin Da Ta Afirka Karo Na 4

Related

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

7 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

9 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

11 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

12 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

14 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

17 hours ago
Next Post
Shanghai: An Gudanar Da Taron Majalisar Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’ummar Sin Da Ta Afirka Karo Na 4

Shanghai: An Gudanar Da Taron Majalisar Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’ummar Sin Da Ta Afirka Karo Na 4

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.