• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Jakadan Nijar A Rasha Ya Mika Wasikar Kama Aiki Ga Shugaba Putin

by Sulaiman
12 months ago
Putin

Shugaban Kasar Rasha Bladimir Putin ya karbi wasikar jakadanci ta sabon jakadan Nijar a kasar Rasha a fadar Kremlin dake Birnin Moscou.

 

Gwamnatin Nijar, a yayin wani zaman taron ministoci na ranar 15 ga watan Mayun shekarar 2024, ta amince da nada Janar Abdou Sidikou Issa a wannan muhimmin matsayi, wanda kuma hakan ya nuna cewa, tsohon shugaban rundunar sojojin Nijar, Janar Abdou Sidikou Issa zai wakilci bangaren diplomasiyyar Nijar a kasar Rasha.

  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje
  • Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

Inda ya mika takardar jakadancinsa ga shugaban Kasar Rasha Bladimir Putin a Nuwamban shekarar 2024.

 

LABARAI MASU NASABA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

Shi dai tsohon manjo-janar din sojojin Nijar, Abdou Sidikou Issa, sananne ne a fagen siyasar Nijar, kuma mutum ne mai son aiki, da ya taka muhimmiyar rawa a lokacin juyin mulkin ranar 23 ga watan Yulin shekarar 2023.

 

Kazalika a 2024, ministan sadarwa Sidi Mohamed Raliou ya gana da dukkan wakilan gidajen rediyo, talabijin da jaridu na kasashen waje dake aiki a Nijar, ganawar da ta gudana a ofishin ma’aikatar sadarwa dake Birnin Yamai.

 

Wannan ganawa irin ta ta farko, ta kasance wani tsarin tattaunawa, da yin musaya kan batutuwa da dama da suka shafi tsinkayen shugaban kwamitin ceton kasa da kuma daidaita matsayin wakilai da aikinsu a Nijar.

 

Ministan sadarwa ya bukaci ganin goyon bayan wakilan kafofin watsa labarai na kasashen waje dake Nijar game da hangen shugaban kwamitin ceton kasa na CNSP Abdourahamane Tiani da ya rataya kan zaman jituwa tsakanin al’ummar kasa, tsaro da kuma mulki na-gari.

 

Haka zalika, minista Sidi Mohamed Raliou ya ja hankalin wadannan ‘yan Nijar dake ma kafafen sadarwa na kasashen waje aiki a Nijar, da su kasance masu kishin kasa, da su sanya moriyar kasarsu a gaba, da kuma fifita ci gaban kasarsu.

 

A nasu bangare, mahalarta wannan ganawa sun nuna jin dadi da gamsuwarsu game da wannan tunani na ma’aikatar sadarwa bisa ga shirya wannan haduwa.

 

Haka kuma, sun yi amfani da wannan dama, domin bayyanawa minista Sidi Mohamed Raliou, matsalolin da suke fuskanta game da neman labarai daga wajen hukumomi, da kuma fatan ganin an daidaita wadannan matsaloli.

 

Daga karshe, minista Sidi Mohamed Raliou, ya tabbatarwa wadannan ‘yan jarida niyyarsa na rakiyarsu da kuma kasancewa mai saurarensu a kowane lokaci, tare da yin musanya kan batutuwan da za su taimaka musu tafiyar da aikinsu cikin sauki kuma cikin girmama ka’idodin aikin jarida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal
Labarai

Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

November 8, 2025
Next Post
Shanghai: An Gudanar Da Taron Majalisar Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’ummar Sin Da Ta Afirka Karo Na 4

Shanghai: An Gudanar Da Taron Majalisar Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’ummar Sin Da Ta Afirka Karo Na 4

LABARAI MASU NASABA

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Yadda Ake Miyar Margi

Yadda Ake Miyar Margi

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Maganin Nankarwa (4)

Maganin Nankarwa (4)

November 8, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.