• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Jakadan Nijar A Rasha Ya Mika Wasikar Kama Aiki Ga Shugaba Putin

by Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Sabon Jakadan Nijar A Rasha Ya Mika Wasikar Kama Aiki Ga Shugaba Putin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasar Rasha Bladimir Putin ya karbi wasikar jakadanci ta sabon jakadan Nijar a kasar Rasha a fadar Kremlin dake Birnin Moscou.

 

Gwamnatin Nijar, a yayin wani zaman taron ministoci na ranar 15 ga watan Mayun shekarar 2024, ta amince da nada Janar Abdou Sidikou Issa a wannan muhimmin matsayi, wanda kuma hakan ya nuna cewa, tsohon shugaban rundunar sojojin Nijar, Janar Abdou Sidikou Issa zai wakilci bangaren diplomasiyyar Nijar a kasar Rasha.

  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje
  • Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

Inda ya mika takardar jakadancinsa ga shugaban Kasar Rasha Bladimir Putin a Nuwamban shekarar 2024.

 

Labarai Masu Nasaba

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Shi dai tsohon manjo-janar din sojojin Nijar, Abdou Sidikou Issa, sananne ne a fagen siyasar Nijar, kuma mutum ne mai son aiki, da ya taka muhimmiyar rawa a lokacin juyin mulkin ranar 23 ga watan Yulin shekarar 2023.

 

Kazalika a 2024, ministan sadarwa Sidi Mohamed Raliou ya gana da dukkan wakilan gidajen rediyo, talabijin da jaridu na kasashen waje dake aiki a Nijar, ganawar da ta gudana a ofishin ma’aikatar sadarwa dake Birnin Yamai.

 

Wannan ganawa irin ta ta farko, ta kasance wani tsarin tattaunawa, da yin musaya kan batutuwa da dama da suka shafi tsinkayen shugaban kwamitin ceton kasa da kuma daidaita matsayin wakilai da aikinsu a Nijar.

 

Ministan sadarwa ya bukaci ganin goyon bayan wakilan kafofin watsa labarai na kasashen waje dake Nijar game da hangen shugaban kwamitin ceton kasa na CNSP Abdourahamane Tiani da ya rataya kan zaman jituwa tsakanin al’ummar kasa, tsaro da kuma mulki na-gari.

 

Haka zalika, minista Sidi Mohamed Raliou ya ja hankalin wadannan ‘yan Nijar dake ma kafafen sadarwa na kasashen waje aiki a Nijar, da su kasance masu kishin kasa, da su sanya moriyar kasarsu a gaba, da kuma fifita ci gaban kasarsu.

 

A nasu bangare, mahalarta wannan ganawa sun nuna jin dadi da gamsuwarsu game da wannan tunani na ma’aikatar sadarwa bisa ga shirya wannan haduwa.

 

Haka kuma, sun yi amfani da wannan dama, domin bayyanawa minista Sidi Mohamed Raliou, matsalolin da suke fuskanta game da neman labarai daga wajen hukumomi, da kuma fatan ganin an daidaita wadannan matsaloli.

 

Daga karshe, minista Sidi Mohamed Raliou, ya tabbatarwa wadannan ‘yan jarida niyyarsa na rakiyarsu da kuma kasancewa mai saurarensu a kowane lokaci, tare da yin musanya kan batutuwan da za su taimaka musu tafiyar da aikinsu cikin sauki kuma cikin girmama ka’idodin aikin jarida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babbar Majalisar Dokokin Kasar Sin Ta Yi Allah Wadai Da Abin Da Ake Kira Dokar Yankunan Teku Na Philippines

Next Post

Shanghai: An Gudanar Da Taron Majalisar Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’ummar Sin Da Ta Afirka Karo Na 4

Related

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar
Labarai

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

4 hours ago
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo
Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

5 hours ago
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

9 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

10 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

12 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

13 hours ago
Next Post
Shanghai: An Gudanar Da Taron Majalisar Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’ummar Sin Da Ta Afirka Karo Na 4

Shanghai: An Gudanar Da Taron Majalisar Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’ummar Sin Da Ta Afirka Karo Na 4

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.