• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sashen Raya Al’Adu Da Yawon Shakatawa Na Kasar Sin Na Kara Ingiza Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A yau Laraba 24 ga watan Agusta, sashen watsa bayanai na JKS, ya gudanar da taron manema labarai, inda a yayin taron aka bayyana cewa, tun bayan taron wakilan JKS karo na 18 da aka gudana yau shekaru 10 da suka gabata, sashen raya al’adu da yawon shakatawa na kasar Sin, ke kara ingiza bunkasuwar tattalin arzikin kasar.

Kaza lika sashen ya zamo sabon karfi dake taka muhimmiyar rawa wajen ingiza sauye-sauye da daga matsayin tattalin arzikin kasar Sin, da kara kyautata nagarta, da biyan bukatun rayuwar al’ummar kasar.

  • Sin Ta Bayyana Kalaman Jakadan Amurka A Sin A Matsayin Shaidar Dake Nuna Tunani Irin Na Danniya

Da yake karin haske game da hakan, babban darakta mai kula da ci gaban masana’antu, a ma’aikatar raya al’adu da yawon shakatawa ta Sin Miao Muyang ya ce, Sin ta kaddamar da sabbin matakai da dama, na bunkasa sashen raya al’adu da yawon shakatawa.

Da farko, fannin masana’antun yana ta kara fadada, kana kasuwar fannin na kara samun tagomashi.

Na biyu, ana kara samun fadadar hidimomin sashen, kuma dunkulewar sassan masana’antun bangaren na ingiza damar cin gajiya daga sashen.

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Na uku, kudaden jari da na hada hadar cinikayya a sashen na karuwa, yayin da ake kara samun manyan nasarori a cinikayyar waje ta fannin.

Na hudu, gwamnati ta ci gaba da fadada matakan tallafawa fannin, ta yadda zai iya kaiwa ga jure mummunan tasirin annobar COVID-19.

A nasa bangare, mataimakin ministan ma’aikatar raya al’adu da yawon shakatawa Rao Quan ya ce, tun bayan taron wakilan JKS karo na 18 da aka gudana yau shekaru 10 da suka gabata, an ga babban tasirin gajiyar da aka samu daga fannin yawon shakatawar yankunan karkarar kasar Sin, wanda shi ma ya zama wani muhimmin bangare na farfadowar yankunan karkarar kasar.

Karkashin wannan nasara, kauyuka kamar su Shibadong na lardin Hunan, da Huamao na yankin Zunyi a lardin Guizhou, sun cimma nasarar kawar da talauci da samun guraben ayyukan yi ta hanyar yawon bude ido.

Bisa wannan nasara ne ma, aka ayyana kauyukan Yucun na lardin Zhejiang, da kauyen Xidi na lardin Anhui, a matsayi na farko a duniya, ta fuskar yawon shakatawa na yankunan karkara, wanda hakan ya zamewa kasar Sin muhimmin abun alfahari da take gabatarwa duniya. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
Daga Birnin Sin

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
Next Post
Wasu Ayyuka Tara Za Su Bunkasa Ci Gaban Hadin Gwiwar Sin Da Afrika Ta Kowacce Fuska

Wasu Ayyuka Tara Za Su Bunkasa Ci Gaban Hadin Gwiwar Sin Da Afrika Ta Kowacce Fuska

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.