• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saudiyya Da Iran Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dawo Da Huldar Jakadanci Tare Da Sake Bude Ofisoshin Jakadanci A Tsakaninsu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Saudiyya Da Iran Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dawo Da Huldar Jakadanci Tare Da Sake Bude Ofisoshin Jakadanci A Tsakaninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda kasashen Sin da Saudiyya da Iran suka sanar a ranar Jumma’ar da ta gabata, kasashen biyu wato Saudiyya da Iran, sun cimma matsaya, wadda ta hada da yarjejeniyar dawo da huldar jakadanci da ma sake bude ofisoshin jakadanci da sake tura jakadu a tsakaninsu cikin watanni biyu.

Karamin ministan harkokin wajen kasar Saudiyya, kuma mamba a majalisar ministocin kasar, kana mai ba da shawara kan harkokin tsaro na kasar Musaad bin Mohammed Al-Aiban, shi ne ya jagoranci tawagar kasar ta Saudiyya, yayin da sakataren majalisar kolin tsaron kasar Iran, Admiral Ali Shamkhani ya jagoranci tawagar kasar Iran a lokacin tattaunawar da ta gudana a birnin Beijing, fadar mulki kasar Sin daga ranakun 6 zuwa 10 ga watan Maris, kamar yadda wata sanarwar bangarorin uku da suka hada da kasashen Sin, Saudiyya da Iran suka bayyana.

  • Aikin Hajjin 2023: Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Gwamnatin Saudiyya

Sanarwar ta ce, kasashen Saudiyya da Iran duk sun mika godiyarsu ga kasashen Iraki da Oman, bisa daukar nauyin gudanar da shawarwari da dama tsakanin shekarar 2021 zuwa ta 2022, da kuma shugabanni da gwamnatin kasar Sin da suka dauki nauyin gudanar da shawarwarin, gami da goyon baya da kuma gudummawar da ta kai ga samun nasarar shawarwarin.

Yayin da yake taya bangarorin biyu murnar daukar wani mataki na tarihi, daraktan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin kolin JKS Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan bangarorin biyu wajen samun ci gaba mai inganci kamar yadda aka cimma cikin yarjejeniyar, ta yin aiki don samun kyakkyawar makoma tare da yin hakuri da nuna hikima.

Ita ma MDD ta yi maraba da wannan yarjejeniya da kasashen Saudiyya da Iran din suka cimma ta sake farfado da huldar diflomasiyya a wannan rana, kana ta yaba da rawar da kasar Sin ta taka a wannan lamari. Bugu da kari, kasashen Oman, da Türkiye, da Lebanon, da Iraki da sauran kasashe, sun fitar da sanarwa, inda suka yi maraba da sanarwar hadin gwiwa da bangarorin uku suka fitar.

Labarai Masu Nasaba

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya yi tsokaci kan tattaunawar da aka yi tsakanin kasashen Saudiyya da Iran a nan birnin Beijing, wanda ya samu kulawa sosai daga bangarori daban-daban.

Kakakin ya ce, tare da hadin gwiwar bangarorin da abin ya shafa, tattaunawar da aka yi tsakanin kasashen na Saudiyya da Iran a birnin Beijing, ta haifar da kyakkyawan sakamako. Kasashen Saudiyya da Iran sun fitar da taswira da kuma lokacin da za a bi, wajen kyautata hadin gwiwarsu, wanda ya samar da wani ginshiki mai kyau, na ciyar da hadin gwiwarsu gaba da kuma sake bude wani sabon babi a huldarsu.

Kakakin ya jaddada cewa, kasar Sin ba ta nuna son kai ko kadan a yankin Gabas ta Tsakiya, yana mai cewa, kasar Sin na mutunta matsayin kasashen yankin Gabas ta Tsakiya, kasancewar wannan yanki nasu ne, kuma tana adawa da gasar siyasa a yankin Gabas ta Tsakiya.

Ya kuma bayyana cewa, kasar Sin ba ta da wata niyya, kuma ba za ta nemi cike wani gurbi ba, ko kuma kafa kungiyoyi na musamman, yana mai cewa, kasar Sin a ko da yaushe tana ganin cewa, ya kamata a ko da yaushe, makomar yankin Gabas ta Tsakiya ta kasance a hannun kasashen yankin. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Siminti Na Dangote Ya Samu Gaggarumar Riba Da Bunkasa A 2022

Next Post

Bita Da Karashen Darasi A Kan Kyawon Cika Alkawari Na Annabi (SAW)

Related

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

19 hours ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

20 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

21 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

22 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

23 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

2 days ago
Next Post
Manzon Allah

Bita Da Karashen Darasi A Kan Kyawon Cika Alkawari Na Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.