• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saudiyya Da Iran Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dawo Da Huldar Jakadanci Tare Da Sake Bude Ofisoshin Jakadanci A Tsakaninsu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Saudiyya Da Iran Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dawo Da Huldar Jakadanci Tare Da Sake Bude Ofisoshin Jakadanci A Tsakaninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda kasashen Sin da Saudiyya da Iran suka sanar a ranar Jumma’ar da ta gabata, kasashen biyu wato Saudiyya da Iran, sun cimma matsaya, wadda ta hada da yarjejeniyar dawo da huldar jakadanci da ma sake bude ofisoshin jakadanci da sake tura jakadu a tsakaninsu cikin watanni biyu.

Karamin ministan harkokin wajen kasar Saudiyya, kuma mamba a majalisar ministocin kasar, kana mai ba da shawara kan harkokin tsaro na kasar Musaad bin Mohammed Al-Aiban, shi ne ya jagoranci tawagar kasar ta Saudiyya, yayin da sakataren majalisar kolin tsaron kasar Iran, Admiral Ali Shamkhani ya jagoranci tawagar kasar Iran a lokacin tattaunawar da ta gudana a birnin Beijing, fadar mulki kasar Sin daga ranakun 6 zuwa 10 ga watan Maris, kamar yadda wata sanarwar bangarorin uku da suka hada da kasashen Sin, Saudiyya da Iran suka bayyana.

  • Aikin Hajjin 2023: Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Gwamnatin Saudiyya

Sanarwar ta ce, kasashen Saudiyya da Iran duk sun mika godiyarsu ga kasashen Iraki da Oman, bisa daukar nauyin gudanar da shawarwari da dama tsakanin shekarar 2021 zuwa ta 2022, da kuma shugabanni da gwamnatin kasar Sin da suka dauki nauyin gudanar da shawarwarin, gami da goyon baya da kuma gudummawar da ta kai ga samun nasarar shawarwarin.

Yayin da yake taya bangarorin biyu murnar daukar wani mataki na tarihi, daraktan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin kolin JKS Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan bangarorin biyu wajen samun ci gaba mai inganci kamar yadda aka cimma cikin yarjejeniyar, ta yin aiki don samun kyakkyawar makoma tare da yin hakuri da nuna hikima.

Ita ma MDD ta yi maraba da wannan yarjejeniya da kasashen Saudiyya da Iran din suka cimma ta sake farfado da huldar diflomasiyya a wannan rana, kana ta yaba da rawar da kasar Sin ta taka a wannan lamari. Bugu da kari, kasashen Oman, da Türkiye, da Lebanon, da Iraki da sauran kasashe, sun fitar da sanarwa, inda suka yi maraba da sanarwar hadin gwiwa da bangarorin uku suka fitar.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya yi tsokaci kan tattaunawar da aka yi tsakanin kasashen Saudiyya da Iran a nan birnin Beijing, wanda ya samu kulawa sosai daga bangarori daban-daban.

Kakakin ya ce, tare da hadin gwiwar bangarorin da abin ya shafa, tattaunawar da aka yi tsakanin kasashen na Saudiyya da Iran a birnin Beijing, ta haifar da kyakkyawan sakamako. Kasashen Saudiyya da Iran sun fitar da taswira da kuma lokacin da za a bi, wajen kyautata hadin gwiwarsu, wanda ya samar da wani ginshiki mai kyau, na ciyar da hadin gwiwarsu gaba da kuma sake bude wani sabon babi a huldarsu.

Kakakin ya jaddada cewa, kasar Sin ba ta nuna son kai ko kadan a yankin Gabas ta Tsakiya, yana mai cewa, kasar Sin na mutunta matsayin kasashen yankin Gabas ta Tsakiya, kasancewar wannan yanki nasu ne, kuma tana adawa da gasar siyasa a yankin Gabas ta Tsakiya.

Ya kuma bayyana cewa, kasar Sin ba ta da wata niyya, kuma ba za ta nemi cike wani gurbi ba, ko kuma kafa kungiyoyi na musamman, yana mai cewa, kasar Sin a ko da yaushe tana ganin cewa, ya kamata a ko da yaushe, makomar yankin Gabas ta Tsakiya ta kasance a hannun kasashen yankin. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Siminti Na Dangote Ya Samu Gaggarumar Riba Da Bunkasa A 2022

Next Post

Bita Da Karashen Darasi A Kan Kyawon Cika Alkawari Na Annabi (SAW)

Related

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

8 hours ago
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

9 hours ago
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

10 hours ago
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

11 hours ago
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

12 hours ago
An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

13 hours ago
Next Post
Manzon Allah

Bita Da Karashen Darasi A Kan Kyawon Cika Alkawari Na Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.