Bankin Zenith ya rufe wasu rassansa da ke babban birnin tarayya Abuja da wasu jihohin kasar nan sakamakon hare-haren da ake kai wa wasu rassansa.
Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) wanda ya sanya ido a kan wasu rassan bankin a FCT da kewaye da wasu jihohi a ranar Talata, ya gano cewa an kulle wasu rassa.
A reshen bankin Zenith da ke kan titin Nyanya Mararaba, kofar shiga bankin da dakin ATM na bankin duk a kulle suke, babu kwastama a wajen.
Wani jami’in bankin da ya so a sakaya sunansa ya bayyana cewa an kuma rufe wasu rassan bankin ne sabida rashin sabbin takardun kudi a bankin.
Jami’in ya bayyana cewa kwastomominsu ne suka kai wa da yawa daga cikin rassansu da ke fadin kasar nan hari wadanda suka kasa cire sabbin takardun kudin daga asusunsu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp