• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Karya Fure Take Ba Ta ‘Ya’ya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi: Karya Fure Take Ba Ta ‘Ya’ya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jama’a, ko kun sha karanta rahotanni da ke cewa, wai “Jarin da kasar Sin ke zubawa Nijeriya suna haifar da matsalar bashi a kasar”, ko “Hadin gwiwa da ke tsakanin Sin da Afirka sabon salon mulkin mallaka ne da kasar Sin ta aiwatar a Afirka”, ko “Bunkasuwar kasar Sin barazana ce ga duniya”? Bayan kun karanta, ko ku ma kuna kallon kasar Sin a matsayin mummunar kasa, har ma kun fara nuna shakku kan hadin gwiwar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka? Idan abin haka yake, lallai, ya kamata ku yi hankali, sabo da rahotannin ka iya zama na jabu, wadanda ake samarwa karkashin wani shirin doka da ya shafi dala biliyan 1.5.

Kwanan nan, Jan Oberg manazarci a wani asusun nazari na kasar Sweden da ake kira Transnational Foundation for Peace and Future Research, ya fayyace cewa, majalisar dokokin kasar Amurka ta zartas da wani shirin doka a kamanin shekaru 5 da suka wuce, wanda ya yi shirin biyan dala biliyan 1.5 cikin shekaru biyar, a yunkurin horar da ‘yan jarida na kasashen yamma wajen rubuta rahotannin neman shafa wa kasar Sin kashin kaza. Dala biliyan 1.5, ba wani abin mamaki ba ne, ganin yadda kafofin yada labarai na kasashen yamma suka yi ta shafa wa kasar Sin kashin kaza a cikin ‘yan shekarun baya.

  • Babban Jami’in Diplomasiyyar Sin Ya Takaita Abubuwan Da Hadin Gwiwar Sin Da Amurka Ya Kawo
  • Adadin Kudin Musaya Da Sin Ta Adana Ya Kai Dala Biliyan 3238 A Karshen Bara

Ban da haka, gwamnatin Amurka ta kuma yi ta zuba makudan kudade a kasashen ketare, don sayen kungiyoyin da ba na gwamnati ba da ma ‘yan jarida na kasashen, da su rika bata sunan kamfanonin kasar Sin da ma ayyukan da suka gudanar. Misali, a shekarar 2021, jaridar The Herald ta kasar Zimbabwe ta ba da labarin cewa, Amurka ta yi amfani da ofishin jakadancinta dake kasar wajen samar da kudade ga wasu cibiyoyi, domin shirya tarukan karawa juna sani, da sayen rahotannin kafafen watsa labarai masu zaman kan su, kan kudi har dalar Amurka 1000 kan ko wacce makala, inda ake umartar su da su rubuta rahotani suna sukar jarin da kamfanonin Sin ke zubawa a Zimbabwe.

Rashin kunya ne yadda Amurka ta dauki irin wadannan munanan matakai, amma kuma ya kamata mu yi hankali da manufar da take neman cimmawa. Dalilin da ya sa Amurka ke zuba kudade tana sayen ‘yan jarida shi ne, tana bukatar kafofin yada labarai su taimaka mata wajen cimma burinta, ko wajen neman tsoma baki a harkokin wasu ko kuma don wanke kanta daga laifuffukan da ta aikata. Misali a shekarar 2003, kafofin watsa labarai da dama sun yi ta watsa rahotanni wai “Iraki ta mallaki makaman kare dangi”, wanda hakan ya zamawa Amurka wani dalilin ta da yaki. Sai dai binciken da aka gudanar bayan yakin ya shaida cewa, sam babu irin wadannan makamai a kasar ta Iraki, wato rahotannin karya ne.

A yayin da kasar Sin ke dada bunkasa, ita Amurka ta yi kuskure har ta dauki kasar Sin a matsayin babbar abokiyar takarar ta ta farko, lamarin da ya sa ta dauki matakai na dakile kasar Sin daga dukkan fannoni, ciki har da fannin yada labarai. Daga wanke masu tada zaune tsaye a yankin Hongkong daga laifin da suka aikata, zuwa yada karairayi game da jihar Xinjiang, har da shafa wa kamfanonin kasar Sin da ke gudanar da ayyuka a ketare kashin kaza, duka ba su rasa nasaba da kasar Amurka ba. Sai kuma a yayin da Sin da kasashen Afirka suka yi ta inganta hadin gwiwarsu, har kuma aka aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya” yadda ya kamata, tattalin arzikin kasashen da abin ya shafa ya yi ta bunkasa, kuma manyan ababen more rayuwa da ma rayuwar al’ummar kasashen ma sun kyautata. Amma Amurka wadda ta dade tana nuna fin karfi a duniya ba ta ji dadin hakan ba, don haka ma muke ta kara karanta rahotanni da ke shafar “sabon salon mulkin mallaka” da “tarkon bashi” da “barazana daga kasar Sin” a rahotannin da kafofin yada labarai na kasashen yamma suke watsawa.

Labarai Masu Nasaba

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

A cewar Mista Jan Oberg, bai ga barazanar da kasar Sin ke haifarwa Amurka daga manufofin diplomasiyyarta ba, ya ce, kasar Sin ba ta tura jiragen ruwan sojanta zuwa bakin teku na California ko na Florida ba, a akasin haka kuma, kasashen yamma sun “kewaye” kasar Sin da jiragen ruwan sojansu.

Jama’a, ku yi hankali a lokacin da kuke karanta rahotannin da ke shafa wa kasar Sin bakin fenti, sabo da ta yiwu sun shafi shirin dokar nan ta dala biliyan 1.5. Ban da haka, za mu so mu shawarci Amurka da ta maida hankali wajen gudanar da ayyuka masu ma’ana da za su amfani kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa, maimakon furta kalaman banza da karairayi, kana ta taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa tattalin arzikin kasashen.(Lubabatu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Alamun Kotun Ƙoli Za Ta Yi Hukuncin Shari’ar Kano Da Legas Ranar Juma’a

Next Post

Tattaunawa Kan Cin Bashi Ba Tare Da Biya Ba (2)

Related

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 
Daga Birnin Sin

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

12 hours ago
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

13 hours ago
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 
Daga Birnin Sin

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

14 hours ago
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

15 hours ago
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

16 hours ago
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

1 day ago
Next Post
Tattaunawa Kan Cin Bashi Ba Tare Da Biya Ba (2)

Tattaunawa Kan Cin Bashi Ba Tare Da Biya Ba (2)

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.